Sin Ta Kalubalanci Amurka Da Ta Dubi Kanta Game Da Yanayin Kare Hakkin Dan Adam
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Kalubalanci Amurka Da Ta Dubi Kanta Game Da Yanayin Kare Hakkin Dan Adam

byCGTN Hausa
1 year ago
Sin

Game da rahoton da ma’aikatar harkokin wajen kasar Amurka ta gabatar don gane da batun kare hakkin dan Adam na kasa da kasa, wanda ya zargi sauran kasashe da gazawa wajen kare hakkin dan Adam, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Wang Wenbin, ya bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar a yau cewa, rahoton na Amurka, ya zargi yanayin kare hakkin dan Adam na kasashe da yankuna kimanin 200 na duniya, amma bai ambato ita kanta Amurka ba. Don haka Sin ta kalubalanci Amurka, da ta dubi kanta, ta fara da warware matsalarta a wannan fanni.

Wang Wenbin ya bayyana cewa, Amurka na gabatar da rahoton kare hakkin dan Adam na shekara-shekara, amma abubuwan dake shafar kasar Sin a rahoton jita-jita ne kawai domin kulle-kullen siyasa, matakin da Sin din ba za ta amince da shi ba.

  • Kasar Sin Ta Bayyana Tarin Rarar Da Take Da Shi Ta Albarkartun Mai Da Iskar Gas
  • Jami’in Ma’aikatar Wajen Sin Ya Yi Tsokaci Game Da Ziyarar Sakataren Wajen Amurka A Kasar

Har ila yau, Wang Wenbin ya yi nuni da cewa, idan Amurka na matukar mai da hankali ga kare hakkin dan Adam, to kamata ya yi ta daidaita matsalolin bindigogi, da miyagun kwayoyi, da nuna bambancin launin fata, da keta hakkin dan Adam dake faruwa a kasar, kana ta yi la’akari da matsalolin da ta kawo wa yankuna masu fama da rigingimu, ta hanyar tsoma baki, da samar da makamai, da kuma ta da zaune-tsaye.

Ban da wannan kuma, Wang Wenbin ya ce, Sin na fatan Amurka za ta dakatar da rura wutar rikici, ko bata sunan wasu sassa don gane da batun Ukraine, domin hakan ba zai warware rikicin da kasar ke fama da shi ba.

Wang, ya yi tsokacin ne yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa na yau Talata, lokacin da yake amsa tambayoyi game da wasu rahotanni daga bangaren Amurka, masu kunshe da zargin alakar tattalin arziki da musaya tsakanin Sin da kasar Rasha. Game da hakan, Wang Wenbin ya ce, yayin da Amurka ke samar da tarin tallafi ga Ukraine, a daya bangaren ba gaira ba dalili, ta soki halastacciyar musayar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Rasha. Ya ce, “Yin hakan munafurci ne da rashin sanin ya kamata, kuma Sin na matukar adawa da hakan”.

Bugu da kari, Wang Wenbin ya yi tsokaci game da wasu rahotanni da suka fito daga kasashen Jamus da Birtaniya, game da zargin nan da wasu sassa ke yi wa kasar Sin, na “Barazanar Leken Asiri”. Yayin taron manema labarai na Talatar nan, Wang Wenbin ya ce, ko shakka babu, burin masu zarge-zargen shi ne bata sunan kasar Sin, da dakile kamfanonin kasar, da gurgunta yanayin hadin gwiwa tsakanin Sin da Turai. Kasar Sin na kira ga sassa masu ruwa da tsaki a wannan batu, da su kauracewa wannan manufa ta kulle-kullen siyasa na shafawa kasar Sin bakin fenti.(Zainab Zhang&Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7
Daga Birnin Sin

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa
Daga Birnin Sin

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Next Post
Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Fitar Da Miliyan 309.5 Don Tallafawa Ɗaliban Da Ke Karatu a Ƙasashen waje 

Gwamnan Jihar Kebbi Ya Amince Da Fitar Da Miliyan 309.5 Don Tallafawa Ɗaliban Da Ke Karatu a Ƙasashen waje 

LABARAI MASU NASABA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version