CRI Hausa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home DAGA BIRNIN SIN

Sin Ta Taya Ngozi Okonjo-Iweala Murnar Zama Babbar Daraktar WTO

by CRI Hausa
February 16, 2021
in DAGA BIRNIN SIN
1 min read
Sin Ta Taya Ngozi Okonjo-Iweala Murnar Zama Babbar Daraktar WTO
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Ma’aikatar cinikayyar kasar Sin, ta taya Ngozi Okonjo-Iweala daga tarayyar Najeriya, murnar zama sabuwar babbar daraktar kungiyar cinikayya ta duniya WTO.

Cikin wata sanarwa da ma’aikatar ta fitar, ta ce Okonjo-Iweala, ta taka rawar gani wajen tallafawa ayyukan yaki da fatara a kasashe masu tasowa, ta kuma yi ayyuka masu nasaba da bunkasa rigakafi da na kiwon lafiya, tana kuma da kwarewar jagoranci, a harkokin gudanar da hukumomin kasa da kasa. Sanarwar ta kara da cewa, nadin na ta, ya dace da hasashen dukkanin sassa.
Kaza lika sanarwar ta ce, duk da annobar COVID-19 da kalubalen da tsarin cinikayyar duniya ke fuskanta, Sin na da cikakken karfin gwiwar cewa, Okonjo-Iweala za ta cimma nasarar sauke nauyin jagorancin kungiyar WTO, tare da taka rawar gani wajen aiwatar da matakan hadin gwiwar yaki da COVID-19, da farfado da tattalin arzikin duniya.
Bugu da kari, sanarwar ta ce, a matsayin ta na kasa mai tasowa mai sauke nauyin dake wuyanta, kasar Sin na goyon bayan tsarin cudanyar cinikayyar duniya, za ta kuma taka muhimmiyar rawa a ayyukan WTO, da gyaran fuskar da ake fatan yiwa kungiyar, za ta kuma yi aiki tare da sabuwar babbar daraktar kungiyar, ta yadda hakan zai taimakawa WTOn aiwatar da gudummawar da za ta inganta jagorancin duniya, da kare moriyar al’ummun sassan duniyar daban daban. (Mai fassarawa: Saminu daga CRI Hausa)

SendShareTweetShare
Previous Post

Nadin Ngozi Okonjo Iweala Matsayin Shugabar WTO, Sanya Kwarya Ne A Gurbinta

Next Post

A Karon Farko Kwararrun WHO Sun Jinjinawa Sin Game Da Tallafinta Ga Binciken Da Suka Gudanar

RelatedPosts

Sabon Nau’in Rigakafin Cutar COVID-19 Da Sin Ta Samar Zai Taimaka Wajen Yakar Cutar

Sabon Nau’in Rigakafin Cutar COVID-19 Da Sin Ta Samar Zai Taimaka Wajen Yakar Cutar

by CRI Hausa
7 hours ago
0

Daga CRI Hausa Shugaban cibiyar kandagarki da shawo kan cututtuka...

Yadda Shugaba Xi Jinping Yake Ba Da Jagoranci Ga Aikin Kula Da Lardin Qinghai

Yadda Shugaba Xi Jinping Yake Ba Da Jagoranci Ga Aikin Kula Da Lardin Qinghai

by CRI Hausa
7 hours ago
0

Daga CRI Hausa A jiya Lahadi, shugaba Xi Jinping na...

Shaidu Sun Karyata Jita-Jitar Da Ake Yadawa Game Da Alluran Riga-Kafin Cutar COVID-19 Na Kasar Sin

Shaidu Sun Karyata Jita-Jitar Da Ake Yadawa Game Da Alluran Riga-Kafin Cutar COVID-19 Na Kasar Sin

by CRI Hausa
7 hours ago
0

Daga CRI Hausa Jiya Lahadi, mamban majalisar gudanarwa kana ministan...

Next Post
A Karon Farko Kwararrun WHO Sun Jinjinawa Sin Game Da Tallafinta Ga Binciken Da Suka Gudanar

A Karon Farko Kwararrun WHO Sun Jinjinawa Sin Game Da Tallafinta Ga Binciken Da Suka Gudanar

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version