Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Siyasar Kano: An Gano Dalilin Rikicin Sanata Gaya Da Kawu Sumaila

by Tayo Adelaja
September 17, 2017
in LABARAI, MANYAN LABARAI, RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Nasir S. Gwangwazo, Abuja

Tun gabanin shekara ta 2018 ta kama daga dukkan alamu siyasar jihar Kano ta fara kamawa da wuta, inda sanata mai kula da Kano Ta Kudu kuma tsohon gwamnan jihar, Alhaji Kabiru Gaya, da tsohon dan majalisar tarayya kuma wakilin mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin majalisar wakilai, Alhaji Kawu Sumaila, su ka saka zare.

samndaads

Da yawan mutane sun a daukar cewa, rikicin na kwanan nan ne lokacin da Kawu Sumaila ya yiwa Sanata Gaya tonon silili a kafafen yada labarai na Kano cewa, a matsayin sanatan na shugaban kwamitin kasafin kudi na majalisa ya rage kudin da gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta ware, don cigaba da aikin titin Kano zuwa Maiduguri, lamarin day a ce ya sanya Buhari mummunan bacin rai a lokacin da ya ke jinya a Turai.

To, amma ashe amma a zahirin gaskiya ba kwanan nan a ka soma wannan rigima ba. Ta samo asali ne tun gabanin manyan zabukan 2015, inda Kawun ya ke zargin Gaya da yi ma sa dungu a lokacin da tsohon gwamnan jihar, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, a ke zargin ya yiwa shi Kawun manakisar tsayawa takara a wancan lokacin, inda ya yi biyu-babu; bai koma majalisar wakilai ba, bai samu takarar gwamna ba kuma sannan ba a ba shi takarar mataimakin gwamna ba.

To, amma bayan da mai ‘takalmin karfe’ ya ballatsewa Kawu, sai a ke zargin cewa Gaya ya ki yarda ya juya wa Kwankwaso baya tunda shi an riga an dawo ma sa da takararsa ta sanata, amma shi Kawu a ka hana shi komawa mukaminsa na dan majalisa.

Bayanai sun nuna cewa, tun daga wannan lokaci ne Hon Kawu ya kullaci Sanata Gaya, kuma ya yanke shawarar neman kujerarsa a zaben 2019 mai gabatowa.

Wakilinmu ya nemi jin ta bakin sanatan da kuma tsohon dan majalisar, amma hakan ya ci tura, saboda majalisa tan a hutu. Amma idan da hali za mu cigaba da bibiyar batun.

SendShareTweetShare
Previous Post

Sharar Fage Daga Alkalamin Edita

Next Post

An Kalubalanci Manoman Nasarawa Game Da Ilimin Kwamfuta

RelatedPosts

Zaben Dan Majalisa

Za A yi Zaɓen Gwamnan Anambara Ranar 6 Ga Nuwamba – INEC

by Sulaiman Ibrahim
1 hour ago
0

HUKUMAR Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa a ranar...

Gina Hanyar Ruwa: Babu Kudin Kowa A Cikin Wannan Babban Aiki, Inji Mai Turaka

Gina Hanyar Ruwa: Babu Kudin Kowa A Cikin Wannan Babban Aiki, Inji Mai Turaka

by Daurawa Daurawa
5 hours ago
0

Mai taimakawa gwamna Masari akan wayar da kan jama’a akan...

Beli

Ka Sake Ba Ni Beli – Maina Ga Alkali

by Muhammad
8 hours ago
0

Ya Ce, Da Gaske Ba Shi Da Lafiya Daga Khalid...

Next Post

An Kalubalanci Manoman Nasarawa Game Da Ilimin Kwamfuta

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version