Mahdi M Muhammad">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home JAKAR MAGORI

Sojoji Sun Mika Wa ’Yan Sanda Mutum Hudu Bisa Zargin Aikata Fashi

by Mahdi M Muhammad
February 17, 2021
in JAKAR MAGORI
2 min read
Sojoji Sun Mika Wa ’Yan Sanda Mutum Hudu Bisa Zargin Aikata Fashi
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Kwamandan runduna ta 13 ta sojojin Nijeriya, Birgediya Janar Mohammed A. Abdullahi, ya mika wasu mutane hudu da ake zargin ‘yan fashi da makami ne ga rundunar ‘yan sandan Nijeriya a kalaba.

Abdullahi ya gabatar da wadanda ake zargin ne a hedikwatar rundunar da ke Kalaba a ranar Litinin, inda Manjo Stanley N. Ikpeme wanda ya wakilce shi, ya ce, binciken ya biyo bayan bin diddigin mutum takwas ne da ake zargi.
Ikpeme ya bayyana cewa, wadanda ake zargin sun yiwa Mista Akan Udoh fashin kudi har Naira 25,000.
Wanda ake zargi na hudu da aka mika wa ‘yan sanda, Peter Obri, an cafke shi da karamar bindiga a gonar dabino a Biase, yayin da wanda yake tare da shi, Bassey har yanzu ba a gano shi ba.
“Mutum na uku da ake zargi, Micah Edet, Bassey Udoh da Emmanuel Bassey, mambobin NSCDC da ke aiki da OP Akpakwu ne suka kama su a ranar 8 ga Fabrairu, 2021, saboda yi wa Mista Akan fashin rana ta Naira 25,000. A lokacin bincike, an gano cewa akwai wani mahallin da wadanda ake zargin suka mayar wurin boyarsu, inda suke kwana da dare,” in ji shi.
Ya ci gaba da cewa, “Haka zalika, Peter Obri, mai shekaru 25, an kame shi a ranar 13 ga Janairun 2021 a gonar Ibiae Rubber tare da karamar bindigar ta kirar gida a yayin da yake kokarin satar ‘ya’yan itacen dabino.”
Ya ce, an mika wadanda ake zargin ga rundunar ‘yan sanda ta Jihar Kuros Riba don ci gaba da bincike tare da hukunta su.
A cikin ikirarinsu, daya daga cikin wadanda ake zargin, Peter Obri, ya ce bai san cewa za su je gonar don yin fashin ba ne, kuma ya kasance tare da abokansa ne kawai.
“Wani abokina ya ce, na raka shi ya dauki wani abu, wnada zai zama banga ne, inda ya ajiye kuma a kan hanyarmu ya ba ni wannan karamar bindiga kirar gida. Na tambaye shi abin da yake son amfani da shi sai ya ce kawai ya rike min. Lokacin da muka isa wurin, ba mu ga banga ba, kuma abin da ba mu sani ba sojoji sun yi mana kwanton bauna, kuma sun kama ni yayin da abokina ya tsere. Ni dan acaba ne, kuma ban san dalilin da ya sa ya nemi in rike masa bindiga ba,” in ji shi.

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Barayi Sun Sace Sassan Mota, Sun Bar Kangarwarta

Next Post

Garkuwa Da Daliban Kagara: Ba Zan Bada Fansar Ko Sisi Ba –Gwamnan Neja

RelatedPosts

Yadda Wasu Tsoffin Fursunoni Suka Sake Tafka Ta’asa

Yadda Wasu Tsoffin Fursunoni Suka Sake Tafka Ta’asa

by Mahdi M Muhammad
4 days ago
0

Daga Mahdi M Muhammad A ranar Litinin da ya gabata...

An Damke Wani Dan Fashi A Nasarawa

An Damke Wani Dan Fashi A Nasarawa

by Mahdi M Muhammad
4 days ago
0

Daga Mahdi M Muhammad Kakakin rundunar, ASP Ramhan Nansel, ya...

Makanike

Wani Mutum Ya Soke Makwabcinsa Da Kwalba

by Mahdi M Muhammad
4 days ago
0

Daga Mahdi M Muhammad Rundunar ‘yan sandan reshen jihar Legas...

Next Post
Daliban Kagara

Garkuwa Da Daliban Kagara: Ba Zan Bada Fansar Ko Sisi Ba –Gwamnan Neja

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version