Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RIGAR 'YANCI

Su Sanata Gaya Sun Halarci Sadakar Kwana 40 Na Surukarsa A Ankpa

by Sulaiman Ibrahim
February 25, 2021
in RIGAR 'YANCI
1 min read
Su Sanata Gaya Sun Halarci Sadakar Kwana 40 Na Surukarsa A Ankpa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Ahmed Muh’d Danasabe, Lokoja

Ranar Lahadi da ta gabata ne garin Ankpa dake Jihar Kogi ya cika makil da jama’a, inda mashahuran mutane ciki har da ’yan siyasa suka hallara a garin, domin halartar sadaka da addu’ar kwana arba’in da rasuwar mahaifiyar sananniyar ’yar siyasar nan, Hajiya Halima Alfa, wato Marigayiya Hajiya Hauwa Kadiri.
Sanata mai wakiltar Kano ta Kudu, Sanata Kabir Ibrahim Gaya, da mataimakin shugaban majalisar dokokin jihar Kogi Hon Muhammed Muhammed suna daga cikin wadanda suka halarci Addu’ar.
Babban limamin garin Ankpa kuma shugaban majalisar malamai na jihar Kogi, Sheikh Salman Adam, wanda ya jagoranci addu’ar, ya karanto wasu surori daga cikin Alkur’ani mai tsarki da Hadisi, inda ya roki Allah (SWT) da ya gafarta wa Marigayiya Hajiya Hauwa Kadiri da kuma yi mata Addu’ar samun rahamar Allah.
Wakilimmu ya ruwaito cewa maigidan Hajiya Halima Alfa, kuma dan majalisa mai wakiltar Kano ta Kudu, Sanata Kabir Ibrahim Gaya da yayansa, wato Tukur Kabir Gaya da Faisal Kabir Gaya da kuma tsohon shugaban karamar hukumar Ijumu, Barista Fadile sun halarci Addu’ar.
Da yake jawabi ga manema labarai kadan bayan gudanar da Addu’ar, Sanata Kabir Ibrahim Gaya, ya bayyana marigayiya Hajiya Hauwa Kadiri a matsayin mutumiyar kirki wacce tayi rayuwa abin koyi.
Ya ce rasuwar Hajiya Hauwa Kadiri, babban rashi ne ga iyalan gidan Eneojo da kuma garin Ankpa baki daya.
A don haka yayi Addu’ar Allah ya yafe mata kurakuranki da kuma saka mata da Aljanna Firdausi.
Addu’ar kwana 40 na marigayiya Hajiya Hauwa Kadiri, wanda aka gudanar a harabar gidan iyalan Eneojo dake garin Ankpa a jihar Kogi, ya samu tubarrakin shugaban karamar hukumar Ankpa, Hon Ibrahim Abagwu da Katukan Lokoja, Hon Bala Salisu da sarakunan gargajiya da kuma ’yan siyasa.

SendShareTweetShare
Previous Post

Yadda Zulum Ya Ziyarci Wadanda Harin Boko Haram Ya Rutsa Da Su A Maiduguri 

Next Post

Za Mu Yi Amfani Da Noma Don Bunkasa Arzikin Kwara – Gwamna Abdulrazak

RelatedPosts

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

by Sulaiman Ibrahim
2 weeks ago
0

Daga Abdullahi Muh’d, Kano Shugaban Gidauniyar ‘Charity’ mai rajin tallafa...

APC

Sanata Al-Makura Ya Cancanci Rike Kujerar Shugabancin APC, Inji Gwamna Sule

by Muhammad
2 weeks ago
0

Daga Zubairu M Lawal, A yayin da uwar jam'iyyar APC...

Jirgin Ruwa

Bagudu Ya Bukaci ’Yan Nijeriya Su Zama Masu Kishin Kasa A Shafukan Sada Zumunta

by Muhammad
2 weeks ago
0

Daga Umar Faruk, Gwamnan Jihar Kebbi Abubakar Atiku Bagudu, a...

Next Post
Za Mu Yi Amfani Da Noma Don Bunkasa Arzikin Kwara – Gwamna Abdulrazak

Za Mu Yi Amfani Da Noma Don Bunkasa Arzikin Kwara – Gwamna Abdulrazak

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version