Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

Sulhu Da Masu Garkuwa: Gwamnatin Zamfara Ta Amso Mata Takwas Da ‘Ya’yansu

Mahara 11 Sun Mika Bindigoginsu

by Sulaiman Ibrahim
February 25, 2021
in LABARAI
2 min read
Sulhu Da Masu Garkuwa: Gwamnatin Zamfara Ta Amso Mata Takwas Da ‘Ya’yansu
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Hussaini Yero, Gusau

A shirin Gwamnatin Jihar Zamfara na sasanci da sulhu da ‘yan bindiga masu garkuwa da mutane da satar shanu da gwamnatin Jihar Zamfara ke yi karkashin jagorancin Gwamna Bello Matawalle Maradun yanzu haka gwamnatin ta ‘yanto mata takwas da ‘ya’yansu hudu da masu garkuwa da mutane suka sace a karamar hukumar Bungudu.
A bikin masu wadanda aka ceto, Gwamna Matawalle ya mika godiyarsa ga Allah akan ceto wadannan mata takwas da ‘ya’yan hudu da suka kwashe wata biyu suna hannun mahara a dajin dansadau.
“Kuma shirinmu na sulhu shine alheri na samun zaman lafiya a Zamfara, kuma duk hanyar da zan bi wajen samar da zaman lafiya a Zamfara zan bi. Sukar masu suka ba za ta hana ni sulhu da mahara ba. Tunda addinimu na Musulunci ya yarda da sulhu, mun amshe shi hannu biyu,” inji Gwamna Matawalle.
An sace matan ne da yaran da suke shayarwa a lokacin da su mahara suka shiga kauyen Rugumau dake cikin karamar hukumar Bungudu wata biyu da suka wuce, amma yanzu gwamnatin Zamfara ta amso mata da ’ya’yansu a bisa sulhu da gwamnatin ke yi da su maharan yanzu haka ba tare da biyan kudin fansa ba, kamar yadda ta bayyana.
Kwamishinan Tsaro na Jihar Zamfara, Hon. Abubukar Dauran, ya bayyana cewa, gamsuwa da sulhu da gwamnatin ke yi da su ‘yan bindiga suka gamsu da shirin Gwamna Matawalle ba yaudara ba ne ya sanya suka bada wadannan mata takwas da ‘ya’yan hudu suka kuma mika makamansu ga gwamnati su ‘yan bindiga 11 daya a cikin wannan satin.
Hon Dauran ya kara da cewa, “wannan ya tabbatar mana da cewa, sulhu alheri ne, don ta hanyarsa mun ceto mutane sama da dubu daya a cikin jihar Zamfara har da wadanda ba ma ’yan Jihar ba, kuma ’yan bindiga sama da 50 ne suka tuba suka mika makamansu. Wannan ba karamin alheri ba ne a gare mu.
“Don haka masu adawa da wannan shirin na samar da zaman lafiya lallai ba za mu bar su ba. Jami’an tsaro za su dauki mataki akansu, don ba son cigaban Jihar Zamfara suke ba.”
Tuni dai Gwamna Matawalle Maradun ya mika wa Kwamishinan ‘Yan Sanda, CP Abutu Yaro, bindigogin da su maharan suka bada da alburusai a fadar gidan gwamnati dake Gusau babban birnin jihar Zamfara a jiya Laraba.

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnatin Zamfara Ta Amshi Tubabbun ’Yan Bindiga Uku

Next Post

Yaki Da Talauci Ya Kai Ga Dukkanin Lungu Da Sako Na Al’ummar Sinawa

RelatedPosts

Malamai

Kungiyar Malamai Ta Tallafa Wa ‘Yan Hijira Sun Shirya Taron Bita Na Ramadan

by Muhammad
2 mins ago
0

Daga Mustapha Ibrahim, Kungiyar Hada Kan zauran Malamai da kungiyar...

Zakzaky

Ramadan: El-Zakzaky Ya Raba Tallafin Abinci Ga Mabukata

by Muhammad
6 mins ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad, Shugaban harkar musulunci a Nijeriya (IMN)...

Musulmi

Wajibi Ne Musulmi Su Ajiye Bambancin Akida Dan Hadin Kai Da Samun Zaman Lafiya – Shareef Ishak  

by Muhammad
12 mins ago
0

Daga Muhammad Awwal Umar, An bayyana cewar wajibi ne musulmi...

Next Post
Yaki Da Talauci Ya Kai Ga Dukkanin Lungu Da Sako Na Al’ummar Sinawa

Yaki Da Talauci Ya Kai Ga Dukkanin Lungu Da Sako Na Al’ummar Sinawa

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version