Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home MANYAN LABARAI

Ta Ƙona Shi A Kan Ɓacewar Wando

by Tayo Adelaja
October 6, 2017
in MANYAN LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abdulrazaƙ Yahuza Jere, Abuja

Wani yaro da bai wuce shekara goma da haihuwa ba a duniya ya gamu da fushin matar wansa inda ta rufe ido ta cire Imani ta kwarara masa kalanzir a jiki kana ta ƙyasta ashana saboda y aɓatar da wandon sawa da ta saya masa.

samndaads

Yaron mai suna Chimobi ya sha wannan azabar a hannun matar ne a titin Adenugba da ke Unguwar Agunfoye a yankin Ƙaramar Hukumar Ikorodu da ke Jihar Legas. Matar mai suna Gift Igwe ana zargin ta banka wa yaron wuta ne bayan ta fahimci ya ɓatar da wandon da ta saya masa a yayin da ta nemi ya kawo wandon ya tsaya yana inda-inda.

Rahotanni sun nunar da cewa jami’an ‘yansanda na yankin Igbogbo sun yi awon gaba da Gift tana can tsare a hannunsu domin gudanar da bincike.

Yaron ya bayyana cewa tun da ya zo gidan matar ta hana shi sakat, kuma ɗan’uwan nasa bai sanya shi a makaranta ba ballantana idan ya fita makaranta ya samu sa’ida.

Jami’in hulɗa da jama’a na ‘yansandan yankin, Olarinde Famous ya tabbatar da aukuwar lamarin inda ya ce da zarar sun kammala bincike za a gurfanar da wacce ake zargin a gaban kuliya.

Rahotannin na nunar da cewa yankin na Ikorodu wanda yake samun bunƙasa a kullu yaumin, yana ƙara zama wurin da masu aikata assha ke cin karensu babu babbaka.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Sabuwar Annobar Cuta Ta Ɓarke A Bayelsa

Next Post

Taƙaddamar Ministan Mai Da Shugaban NNPC: Me Majalisa Za Ta Binciko?

RelatedPosts

'Yan Adaidaita

An Sasanta Yajin Aikin ’Yan Adaidaita Bayan… Motocin ‘Kano Line’  Sun Koma Jigilar Jakara-Kasuwa

by Muhammad
1 day ago
0

Babu Hanunmu A Ciki Wannan Yaji – Shugaban ’Yan Adaidaita...

Adaidaita

Yajin Aikin Adaidaita: Acaba Ta Dawo A Kano

by Muhammad
2 days ago
0

Ya Jefa Jama’a Cikin Tsaka Mai Wuya Yadda Aka Koma...

Masu Garkuwa

Tattaunawa Da Masu Garkuwa: Yadda Gwamnonin Kaduna Da Neja Suka Raba Gari

by Muhammad
3 days ago
0

Shin Sheikh Gumi Ne Ya Raba Tsakani? Daga Nasir S....

Next Post

Taƙaddamar Ministan Mai Da Shugaban NNPC: Me Majalisa Za Ta Binciko?

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version