Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home Hannunka Mai Sanda

Ta’aziyya Tare Da Jinjina Ga Marigayi Sam Nda-Isaiah (II)

by Muhammad
December 25, 2020
in Hannunka Mai Sanda
3 min read
Ta'aziyya
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Ci gaba daga makon jiya

Siyasarsa

samndaads

Za a iya cewa, Nda-Isaiah, ya fara aiwatar da manufarsa ta siyasa ne tun a fagen rubuce-rubuce da ya jima yana yi a Jaridu, sai daga baya ne ya fado tsundum cikin fagen siyasar a aikace fafur, musamman lokacin da ake kici-kicin hadakar jam’iyyar APC.

 

 

Cikin sakon ta’aziyyar gwamnan jihar Ogun, Prince Abiodun, ga iyalan Nda, ya tabbatar da cewa, marigayin, na yin siyasa ne da akida, tare da son cigaban al’uma. A aikace, Ndan, ya nuna haka a lokacin da Buhari ya ka da shi a takarar da ya yi. Bai ta da rikici ba, bai ce, sai shi ne kadai ba ya cancanta a zaba. Ta tabbata shi ne ma ya jagoranci bangaren yada labarai na takarar Buharin, har zuwa lokacin da aka sami nasara. Ga shaidar kyakkyawan salon siyasar tasa da gwamna Abiodun ke shelantawa;

 

“…The country has lost a rare gem of big ideas, whose politics was laced with conbiction, selflessness and without bitterness. Iam still in shock. I was jolted by the news”.

 

Ga fassarar kalaman;

 

 

Ta tabbatar marigayi Nda, na yin gwagwarmayar siyasa ne kadai, don son ganin rayuwar al’uma ta inganta, ba don zari ko halayya ta cinye-du ba!!!.

 

“…Sam Nda-Isaiah was a resolute and dogged fighter on the side of the people…”.

 

Ogun State Gobernor

 

Cikin Harshen Hausa, ga abinda gwamnan ke cewa;

 

“…Sam Nda-Isaiah kuwa, ya kasance dan gwagwarmaya mai kwazo, a kullum ba ya kosawa cikin fafutukar kwatowa al’uma hakkokinsu…”.

Kyankyasar Jaridar Leadership

A karshe, babu shakka al’umar Najeriya manyansu da kananansu, na masu mika sakon ta’aziyyarsu ga Iyalai, “yan’uwa, ma’aikatan gidan Jaridar ta Leadership, jihar Niger da ma sauran al’umar Kasar nan bakidaya, bisa rasuwar wannan Dan Kishin Kasa, Sam Nda-Isaiah, Aare Baaroyin na masaraurar Akure, bisa katafariyar gudunmuwar da ya bayar tsawon lokaci ga mabanbantan fagage na rayuwa cikin wannan Kasa. Mu na masu fatan kyawawan ayyukansa su bi shi, tare da zame masa manyan gwala-gwalen nasara cikin wannan Duniya da muke ciki.

Kammalawa.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Waiwayen Kanun Labaru: Daga Litinin 6 Zuwa Alhamis 9 Ga Jimada Ula 1442, Bayan Hijira

Next Post

Waiwaye A Kan Wasu Ayyukan NIS A Filin Jiragen Sama Na Abuja A 2020

RelatedPosts

Ababen Hawa

Batun Yawaitar Haduran Ababen Hawa A Nijeriya (I)

by Sulaiman Ibrahim
6 days ago
0

Saboda yau da gobe, sai ya zamana cewa, ba mutane...

Shekarar

Fatan Alheri A Sabuwar Shekarar Miladiyya Ta 2021 (II)

by Muhammad
2 weeks ago
0

Bazuwar Ayyukan Ta'addanci Da Afkuwar Rikice-Rikice A Kasa Babu shakka...

Kasafin 2021: Ya Takura Ilimi Da Kiwon Lafiya

Kasafin 2021: Ya Takura Ilimi Da Kiwon Lafiya

by Sulaiman Ibrahim
3 weeks ago
0

Inganta tsarin ilimi da kiwon lafiya su ne abubuwa mafi...

Next Post
Filin Jirgi

Waiwaye A Kan Wasu Ayyukan NIS A Filin Jiragen Sama Na Abuja A 2020

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version