Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home TATTALIN ARZIKI

TAJBank Na Kokarin Inganta Harkokin Ilimi A Nijeriya

by Muhammad
January 26, 2021
in TATTALIN ARZIKI
2 min read
TAJBank
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Bankin TAJBank wanda yake gudanar da kasuwancinsa ta tare da kudin ruwa ba, ya jaddada cewa yana kokarin inganta ilimi a Nijeriaya. Wannan ya zo a dai-dai lokacin da aka kaddamar da sabon makarantar Saint John Paul School da ke cikin Jihar Akwa Ibom.

Ministan Niger Delta, Sanata Godswill Akpabio wanda shi ne babban bako a wajen kaddamar da makarantar, ya yaba wa bankin bisa kadirinta na tallafa wa bangaren ilimi wanda ya bayar da kudade domin samar da ababen more rayuwa a wannan makaranta. Ya kara da cewa, yana kira da sauran bankuna da su yi koyi da bankin wajen tallafa wa ilimi a cikin kasar nan. Akpabio ya bukaci bankin ta yi kokarin bude rashe a a Uyo a duk lokacin da suka sami lasisin bude rassa a ko’iya a fadin duniya.

samndaads

Wakilin bankin a wajen taron, Mista Nasir .T. Usman ya bayyana cewa, shugabannin Saint John Paul School Akwa Ibom sun yi kokarin cike gibin da ake samu a bangaren ilimi a Nijeriya, domin haka sun cancanji a samar musu da abubuwan da suke bukata nan take. Ya bayyana cewa, sakamakon irin shawarwarin da makarantar ta samu a cikin watan tara, sun samu nasarar bai wa dalibai ingantaccen ilimi tun lokacin kafuwarta. Ya kara da cewa, a cikin shakara daya da bankin TAJBank ya samu nasarar cimma nasarori masu tarain yawa.

A cikin ‘yan kwananin nan, bankin ya samu lambar yabo daga kamfanin gudanarwa na jaridar Leadership bisa irin namijin kokari da bankin yake yi a fadin kasar nan a bangaren harkokin kudade musamman ma a kan mutane marasa karfi.

Bankin ya fara gudanar da ayyukansa ne a ranar 4 ga watan Disambar shekarar 2019, wanda a wata da ta gabata ce bankin ya cike shekara daya da kafuwa. A cikin kayayyakin da bankin ya samar a cikin makarantar sun hada da kayayyakin kimiyya da fasaha da kayayyakin rubutu da takardun karatu wanda aka bai wa wannan makaranta domin kara inganta ilimi a cikin jihar.

SendShareTweetShare
Previous Post

Yadda Maza Ke Kaurace Wa Iyalinsu Sanadiyyar Cutar Yoyon Fitsari

Next Post

Gwamnati Za Ta Kashe Biliyan N71 Wajen Kwangilar Titinan Dogo Shida

RelatedPosts

Farashin Dizel Ya Yi Tashin Gwauron Zabi

Farashin Dizel Ya Yi Tashin Gwauron Zabi

by Sulaiman Ibrahim
5 days ago
0

Farashin dizil ya yi tashin gwauron zabi wanda lita daya...

Korona Ta Kawo Tsaikon Kammala Matatar Man Dangote Zuwa 2021

Matatun Man Dangote Za Su karfafa Darajar Naira Da Ceto Tattalin Arziki – Majalisar Wakilai

by Sulaiman Ibrahim
5 days ago
0

Majalisar Wakilan Nijeriya ta bayyana cewa, matatan man kamfanin Dangote...

“Duk Da An Sauya Shugabannin Tsaro, Har Yanzu Da Saura”

Na Shirya Tsaf Don Fitar Da Mutum Miliyan 100 Daga Kangin Talauci – Shugaba Buhari

by Sulaiman Ibrahim
5 days ago
0

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa, burin gwamnatinsa na...

Next Post
Layin Dogo

Gwamnati Za Ta Kashe Biliyan N71 Wajen Kwangilar Titinan Dogo Shida

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version