Rabiu Ali Indabawa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home JAKAR MAGORI

Takwaran Hitler Ya Lashe Zabe A Kasar Namibiya

by Rabiu Ali Indabawa
January 5, 2021
in JAKAR MAGORI
2 min read
Takwaran Hitler Ya Lashe Zabe A Kasar Namibiya
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Wani dan siyasa da aka sanya wa suna bayan sanannen dan siyasar Jamani kuma shugaba, Adolf Hitler ya lashe kujera a zaben Namibiya, amma ya ce ba shi da shirin mamaye duniya.

Mista Adolf Hitler Uunona, wanda aka zaba da kashi 85 cikin 100 na kuri’un, ya fadawa jaridar Bild cewa, “ba shi da wata alaka da akidar ‘yan Nazi(‘yan Hitila). Ya lashe kujerar ne a tikitin jam’iyyar SWAPO mai mulki, wacce ke mulkin Namibia tun samun ‘yancin kai daga Afirka ta Kudu ta wariyar launin fata a 1990.”
Namibia, tsohuwar mulkin mallakar Jamani da aka fi sani da Jamhuriyar Afirka ta Kudu ta Yammacin Afirka, har yanzu tana zaune ne a wurin karancin al’ummar jamani, da karancin tituna, wurare da mutane har yanzu sunaye da Jamani.
Ya ce, “Mahaifina ya sanya min sunan wannan mutumin ne ba tare da sanin abin da Adolf Hitler ya tsaya ma wa ba. A lokacin da ni ke yaro ina ganin sunan ne a matsayin cikakken suna na al’ada. Tun ina saurayi na fahimci cewa wannan mutumin yana son cinye duniya ne baki daya.”
dan siyasan ya ce, matarsa na kiransa Adolf, ya kara da cewa, yawanci ana kiransa ne da Adolf Uunona, amma loakci ya kure da zai sauya sunansa a hukumance.
Ya kara dea cewa, “Kasancewar ina da wannan sunan ba yana nufin ina so in mamaye Oshana ba ne, hakan nufin wurin da na ci zaben ne kawai. Haka zalika, ba yana nufin ina kokarin neman mamayar duniya bane.”
Uunona ya samu kuri’u 1,196 a zaben da ya gabata idan aka kwatanta da 213 ga abokin hamayyarsa, inda ya mayar da shi kan kujerar majalisar yankin wanda a baya ya ci a shekarar 2015. An gajarta sunansa da “Adolf H” a cikin jerin sunayen ‘yan takarar da aka buga a cikin jaridar gwamnati, amma sunansa ya bayyana cikakke akan shafin yanar gizon sakamakon zabe.

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Ya Watsa Wa Matarsa Asid Bisa Kin Abokansa Su Yi Ma Ta Fyade

Next Post

Kamfanonin Jiragen Sama 18 Sun Kasafta Naira Biliyan Hudu Na Tallafi

RelatedPosts

Kyanwa

Kyanwa Ta Rayu Makonni Uku Ba Abinci Da Ruwa  

by Rabiu Ali Indabawa
20 hours ago
0

Wata kyanwa ta baiwa ma'aikatan kamfanin jigilar kaya matukar mamaki...

Kayan Gini

An Garkame Mutane Biyu Da Suka Saci Kayan Ginin Naira Miliyan 200

by Rabiu Ali Indabawa
20 hours ago
0

A ranar Litinin da ta gabata ne wata Kotun Majistare...

Yarinyar

An Ceto Yarinyar Da Iyayenta Suka Kulle Tsawon Shekaru Biyar

by Rabiu Ali Indabawa
20 hours ago
0

An ceto wata yarinya ‘yar shekaru ashirin da haihuwa a...

Next Post
Kamfanonin Jiragen Sama 18 Sun Kasafta Naira Biliyan Hudu Na Tallafi

Kamfanonin Jiragen Sama 18 Sun Kasafta Naira Biliyan Hudu Na Tallafi

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version