Tallafin Da Amurka Ta Baiwa Gaza Wasan Kwaikwayo Ne
  • English
  • Business News
Tuesday, October 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tallafin Da Amurka Ta Baiwa Gaza Wasan Kwaikwayo Ne

byCGTN Hausa
2 years ago
Amurka

Kwanan baya, Isra’ila ta ci gaba da kaiwa zirin Gaza hare-hare, lamarin da ya yi sanadin asarar rayuka da dama. Amurka ce ta samar da da yawa daga cikin makaman da Isra’ila ta yi amfani da su. Bisa labarin da shafin yanar gizo na jaridar kasar Isra’ila wato Ha’aretz ya bayar, an ce, Amurka ta shafe tsawon watanni 5 tana jigilar makamai ta sama zuwa Isra’ila.

A wani bangare Amurka na tallafawa Isra’ila da makamai, yayin da a wani bangare na daban kuwa, ta yanke shawarar jefa wa fararen hula a Gaza abinci daga sama. Sai dai daga cikin dubban abincin da ta jefa, yawancinsu sun fada ne cikin teku, wadanda suka kasa biyan bukatun fararen hular Gaza da yawansu ya haura miliyan 2. Ban da wannan kuma, sakamakon yadda laimar sauka daga jirgin sama masu dauke da abincin sun gaza budewa cikin lokaci, ya sa abincin ya fada kai tsaye kan wasu gidaje da mutane dake kasa, abin da ya sa mutane 5 suka mutu.

  • Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL
  • Jamhuriyar Congo Tana Son Karfafa Zumunta Da Hadin Gwiwa Da Sin

Shin ko da gaske ne Amurka tana mai da hankali kan rikicin jin kai dake faruwa a Gaza?

Kungiyoyin jin kai da dama sun yi tir da hanyar da Amurka ta zaba ta samar da tallafin jin kai ta hanyar jefa abinci daga sama. A ganinsu, a maimakon bukatar kawarta wato Isra’ila da ta bude hanyoyin jin kai, ko daina samarwa Isra’ila makamai, Amurka ta zabi hanyar da ba ta dace ba, wato jefa abinci daga sama, kuma burin da take neman cimmawa shi ne samun goyon baya daga masu kada kuri’u a gida.

Ban da wannan kuma, shugaban kasar Amurka Joseph Biden ya sanar da shirin kafa wata tashar jirgin ruwa ta wucin gadi a gabar tekun bahar Rum dake Gaza, don baiwa yankin tallafin jin kai. Hakan ya jawo suka daga masu bibbiyar kafar sada zumunta ta X, wadanda suka yi zargin cewa, Amurka tana da karfin dakatar da rikicin da ake fuskanta a Gaza muddin ta daina samarwa Isra’ila makamai, amma ta yi wasan kwaikwayo na samar da tallafin jin kai.

Tallafin da Amurka ta bayar da kyar sun isa hannun fararen hula, amma makaman da ta samar sun halaka mutane masu dimbin yawa. ‘Yan siyasar Amurka su kan yi wasan kwaikwayo don samun kuri’u, amma a wannan karo masu gudun hijira ke yin asara, wadanda ba su da abinci ba su da gidaje kuma ba su da tsaro, ballantana hakkin Bil Adama. Shin ko ‘yan siyasar Amurka ba su jin kunya? (Mai zana da rubutu: MINA)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka
Ra'ayi Riga

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

September 30, 2025
Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

September 29, 2025
Next Post
Irin Babban Taron LEADERSHIP ‘Yan Nijeriya Ke Bukata

Irin Babban Taron LEADERSHIP ‘Yan Nijeriya Ke Bukata

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Na Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Korea Ta Arewa

Firaministan Sin Zai Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Na Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Korea Ta Arewa

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version