Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

byCGTN Hausa and Sulaiman
4 weeks ago
Tarihi

A bana ne ake cika shekaru 80 da samun nasarar yakin duniya na kin mafarkin murdiya. Tarihi ya nuna mana cewa, tabbatar da adalci ya kasance alkiblar al’ummar dan Adam ta dindindin. Ko da yake a wani lokaci mugunta ta samu damar mai da hannun agogo baya, amma a karshe abubuwa za su koma daidai.

Sama da shekaru 80 da suka gabata, lokacin da motocin yaki na Jamus suka murkushe kauyuka a kasashen gabashin Turai, kuma jiragen saman yaki na Japan suka jefa bama-bamai a kasar Sin da mai da biranenta zuwa kufai: da alama kasashen sun kasance masu karfi da ba za su taba shan kaye ba. Amma a karkashin turjiyar mutane masu adalci na duniya, ‘yan mulkin zalunci ba za su iya magance faduwar totuwa da fuskantar hukunci a karshe ba. Mugunta ba za ta iya lashe adalci ba, wannan yana cikin ka’idojin tarihi.

  • Ana Zargin Jami’in Sibil Difens Da Harbe Abokin Aikinsa A Abuja
  • Neman Gurbi: Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Afirka Ta Kudu A Bloemfontein

Sai dai har yanzu, bil’adama suna ci gaba da fuskantar ayyukan dake neman mai da hannun agogo baya: tunanin mulkin danniya, da ra’ayi na daukar matakin kashin kai, da na kariyar ciniki, suna yaduwa a duniya. Wasu kasashe sun kaddamar da yakin cinikayya da na haraji, wadanda suka yi matukar illata tattalin arzikin duniya da kuma karya dokokin cinikayya na kasa da kasa. Amma masu kare adalci suna nan a ko da yaushe, wadanda ke kokarin mayar da duniya kan turba mai dacewa, kuma kasar Sin na daya daga cikinsu.

A gun taron kolin BRICS da aka gudanar jiya ta yanar gizo, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da shawarwari guda uku a cikin jawabinsa: Wato tsayawa kan manufar cudanyar sassa daban-daban, da kiyaye daidaito da adalci a duniya; da tabbatar da bude kofa da cin moriya tare, don kare tsarin tattalin arziki da cinikayya na kasa da kasa; da kuma tabbatar da hadin kai a kokarin samun ci gaba na bai daya. Wadannan shawarwari, sun kunshi kalmomi na nuna sassaucin ra’ayi, amma ma’anarsu na cike da adalci. Suna wakiltar martanin kasar Sin game da yunkurin mayar da hannun agogo baya da ake fuskanta a halin yanzu a fagen kasa da kasa, wadanda ke nuna yadda kasar Sin ke tsayawa tsayin daka wajen tabbatar da gaskiya da adalci, da neman hadin kai, da sa kaimi ga tabbatar da moriyar juna a duk fadin duniya. Wannan tsari na adalci shi ne ainihin dalilin da ya sa kasar Sin samun cikakken goyon baya daga mafi yawan kasashen duniya.

Tabbas, ya kamata a kiyaye adalci ta hanyar aikace-aikace maimakon magana. Mu dauki yakin haraji da Amurka ta kaddamar kan Afirka a misali: Bayan da Amurka ta sauya manufarta ta ciniki da kasashen Afirka, da sanya musu harajin fito mai yawa da ya kai kaso 15 zuwa kaso 30 cikin 100, nan da nan kasar Sin ta fara taimakawa kasashen Afirka, inda ta sanar da cewa, za ta yafe dukkan harajin da ake karba kan kayayyakin da kasashe 53 dake nahiyar Afirka, wadanda suka kulla hulda da ita, suka fitar zuwa cikin gidanta. Wannan matakin ya aike da wani sako mai kyau ga Afirka, wato kasar Sin na son raba damar samun ci gaba tare da kasashen Afirka, da hadin kai da su don tinkarar hadurra. Lamarin da ya samu yabo daga masana tattalin arziki na kasashen Afirka.

Kana wasu alkaluman da ma’aikatar kasuwancin kasar Sin ta fitar sun nuna cewa, a cikin watanni 7 na farkon wannan shekara, darajar kayayyakin da kasar Sin ta shigo da su daga kasashe mafi karancin ci gaba a nahiyar Afirka, wadanda Sin ta riga ta yafe musu dukkan haraji, ta kai dalar Amurka biliyan 39.66, adadin da ya karu da kaso 10.2 cikin dari bisa na makamancin lokacin a bara. Ta hanyar karfafa hadin gwiwar cinikayya da abokan hulda kamar Sin, da inganta cinikayya a cikin nahiya, ana sa ran ganin Afirka za ta samu nasarar rage tasirin manufar harajin Amurka.

A halin yanzu, kasashe masu tasowa, ciki har da kasar Sin da kasashen Afirka, suna kokarin daukaka ra’ayin cudanyar sassa daban daban, da na bude kofa, da yin hadin gwiwa tare da tabbatar da moriyar juna, da hadin kai da juna, a karkashin laimar tsare-tsaren hadin gwiwa irin na BRICS, kuma suna tafiya zuwa gaba kan wata turba mai adalci. Tabbas babu wani karfi da zai iya hana su cimma buri da samun nasara. (Bello Wang)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka
Ra'ayi Riga

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

September 30, 2025
Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

September 29, 2025
Next Post
MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

MDD Ta Yi Allah-wadai Da Harin Boko Haram A Bama

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version