Taron MDD: Gwamntin Tarayya Za Ta Dauki Nauyin Gudanar Da Makarantar UNESCO A Nijeriya - Minista
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taron MDD: Gwamntin Tarayya Za Ta Dauki Nauyin Gudanar Da Makarantar UNESCO A Nijeriya – Minista

bySulaiman
2 years ago
Tarayya

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana ƙudirin Gwamnatin Tarayya na buɗe babbar makarantar koyar da aikin jarida da ilimin labarai ta Hukumar Ilimi, Kimiyya da Al’adu ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNESCO Category 2 Institute for Media and Information Literacy) a Nijeriya ba tare da ɓata lokaci ba.

Ministan ya faɗi haka ne a wajen taron ƙasa da ƙasa na Mataimakin Darakta-Janar mai kula da Yaɗa Labarai na UNESCO, Dakta Tawfik Jelassi, a wani sashe na Babban Taro na 42 na hukumar UNESCO a ranar Talata a Paris, babban birnin ƙasar Faransa.

  • Rashin Tsaro: Za Mu Fara Horar Da Jami’an Sa-Kai Don Tsare Al’ummar Zamfara – Gwamna Lawal
  • Wadanne Damammaki Da Aka Samu Cikin Abubuwan Da Aka Nuna A Karon Farko A Duniya A CIIE?

Wannan alƙawari da Nijeriya ta yi na buɗe wa tare da ɗaukar nauyin makarantar, an yi shi ne tun lokacin da aka yi Makon Aikin Jarida da Yaɗa Labarai na Duniya na UNESCO na shekarar 2022, wanda aka yi a Nijeriya cikin Oktoba 2022, a Abuja, wanda kuma aka rattaba hannu kan ƙudirin aikin a Zama na 216 na Babbar Hukumar Gudanarwar UNESCO, cikin Mayu 2023.

Yayin da ya ke ƙara tabbatar da sadaukarwar Nijeriya ga manufofi da burukan UNESCO, Minista Idris ya bayyana cewa duk da yake ƙasar nan ta na shirin sauka daga kujerar ta a Majalisar Ƙasa da Ƙasa ta Shirin Cigaban Harkokin Yaɗa Labarai na Duniya na UNESCO (IPDC), bayan ta shafe shekaru shida a majalisar, to kuma ta na neman zama memba a Majalisar Ƙasa da Ƙasa ta Shirin Samar da Labarai ga Kowa, wato ‘Information for all Programme’ (IFAP).

 

Idris ya sha alwashin cewa, zai tabbatar Nijeriya ta ci moriyar dukkan wasu damarmaki da ke akwai a Sashen Aikin Jarida da Yaɗa Labarai na UNESCO, ciki kuwa har da samar da ƙananan gidajen rediyo na unguwanni, wanda ya na daga cikin tsare-tsaren da UNESCO ta ke ba muhimmanci a yanzu.

Ministan ya kuma bayyana ƙudirinsa na dawo da darajar kafafen yaɗa labarai na gwamnatin Nijeriya, tare da kuma samar da tattaunawar ƙasa gaba ɗaya kan kyawawan ɗabi’u da halayen Nijeriya, a matsayin wani shirin gangamin wayar da kan jama’a da za a yi a duk faɗin ƙasar, wanda ya ce al’amari ne da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta ɗauka da muhimmanci.

Ministan ya gode wa Jakadiya Hajo Sani saboda aiki tuƙuru da ta ke yi na wakiltar burukan Nijeriya a UNESCO, da muhimmiyar rawar da ta taka wajen samar wa Nijeriya damar zama mai masaukin baƙi a Makon Aikin Jarida da Yaɗa Labarai na Duniya na UNESCO na shekarar 2022, da kuma shirye-shiryen da ake yi don ɗaukar nauyin da Nijeriya za ta yi na buɗe babbar makarantar ‘UNESCO MIL Institute’ ta farko a duk duniya.

Da ya ke mayar da jawabi, Mataimakin Darakta-Janar na UNESCO, Dakta Jelassi, ya yaba wa Nijeriya kan babbar rawar da ta ke takawa a UNESCO, sannan ya yi alƙawarin cewa, hukumar za ta ci gaba da mara wa ƙasar baya domin ta ci moriyar dukkan damarmakin da ke akwai na haɓaka ɓangarenta na aikin jarida da yaɗa labarai.

Ya lissafa ayyukan da UNESCO ke aiwatarwa a sassa daban-daban, daga tabbatar da ‘yancin ‘yan jarida a ƙasashen duniya, zuwa tallafawa wajen kafa gidajen rediyo na unguwa, da aikin da ake yi don daidaita ayyukan da ƙasashe ke yi wajen yaƙar baza labaran bogi, da labaran ƙarya da kuma kalaman ɓatanci.

Tun da farko, mai girma Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris, ya na cikin ayarin sauran mahalarta taron daga Nijeriya, ciki har da shugaban tafiyar, wato mai girma Ministan Ilimi, Farfesa Tahir Mamman (wanda kuma shi ne Shugaban Hukumar UNESCO ta Ƙasa), da su ka halarci bikin buɗe Babban Taro na 42 na UNESCO.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Next Post
NLC Da TUC Sun Rufe Titin Zuwa Filin Jirgin Saman Abuja, Sun Bukaci A Hana Zuwa Imo

NLC Da TUC Sun Rufe Titin Zuwa Filin Jirgin Saman Abuja, Sun Bukaci A Hana Zuwa Imo

LABARAI MASU NASABA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version