Tashar Sararin Samaniyar Sin Na Samar Da Sabon Dandalin Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa A Bangaren Kimiyya
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tashar Sararin Samaniyar Sin Na Samar Da Sabon Dandalin Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa a Bangaren Kimiyya

byCGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
Sin

Jiya Laraba da sassafe, kasar Sin ta cimma nasarar harbar kumbo mai suna “Shenzhou-19”, wanda ke dauke da ‘yan sama jannati 3 na kasar, wadanda suka shiga tashar sararin samaniyar Sin lami lafiya. Wannan shi ne ci gaban kimiyya a wannan bangare da kasar Sin ta samu, wanda kuma zai samar da sabon dandali ga hadin gwiwar kasa da kasa dangane da nazarin sararin samaniya.

 

Tuni a shekarar 2019, ofishin kula da harkokin kumbuna masu dauke da mutane na kasar Sin, da ofishin kula da harkokin sararin samaniya na MDD, suka ba da hadaddiyar sanarwar cewa, wasu shirye-shirye 9 daga kasashe 17, sun zama na farko da tashar sararin samaniya ta Sin za ta gudanar ta fannin nazarin kimiyya.

  • An Yanke Wa Mai Haƙar Ma’adanai Hukuncin Shekara 1 Saboda Satar Waya
  • Layuka A Gidajen Mai Za Su Ragu Idan ‘Yan Kasuwa Suka Fara Sayan Mai A Wajenmu – Dangote

Sai kuma a ranar 29 ga watan nan da muke ciki, ofishin kula da harkokin kumbuna masu dauke da mutane na kasar Sin ya sanar da cewa, a karon farko “Shenzhou-19” na maraba da ‘yan sama jannati daga ketare da su shiga ayyukan tashar sararin samaniya ta kasar Sin. Hakan ba wai ya bayyana bude kofa da Sin take yi ba ne kadai, har ma ya samar da sabon dandali ga hadin gwiwar Sin da kasashen duniya a bangaren nazarin kimiyya.

 

A gun taron manema labarai da aka yi a wannan rana kuma, kakakin ofishin kula da harkokin kumbuna masu dauke da mutane na kasar Sin Lin Xiqing, ya nuna ce, “Tashar sararin samaniyar Sin ba kawai za ta amfani kasar ita kadai ba, haka kuma tasha ce da ke gaggauta bunkasuwar fasahohin dan Adam masu alaka da sararin samaniya, wadda kuma ke amfanar da daukacin bil Adam”.

 

Hadin gwiwar kasa da kasa a bangaren harba kumbuna masu dauke da mutane zuwa sararin samaniya, mataki ne da ya zama tabbas a halin yanzu, kuma matsaya daya ce da duk wata kasa dake da niyyar dukufa kan yin amfani da sararin samaniya cikin lumana ke dauka. Ko shakka babu, bunkasuwar kimiyyar sararin samaniya ta kasar Sin, da yadda take bude kofarta a wannan bangare, zai kara ba da gudummawa wajen nazarin sararin samaniya da bil Adama ke gudanarwa. (Mai zane da rubutu: MINA)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?
Daga Birnin Sin

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
Next Post
Magoyin Bayan Manchester United Ya Rasa Ransa A Dalilin Musun Kwallo A Uganda 

Magoyin Bayan Manchester United Ya Rasa Ransa A Dalilin Musun Kwallo A Uganda 

LABARAI MASU NASABA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version