Mustapha Abdullahi">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Tattaunawa Ce Babbar Hanyar Magance Matsalar Tsaron Nijeriya – Bayero Fullo

by Mustapha Abdullahi
February 2, 2021
in LABARAI
1 min read
Tattaunawa Ce Babbar Hanyar Magance Matsalar Tsaron Nijeriya – Bayero Fullo
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Sakataren kungiyar matasan Fulani ta FUSADAN, Bala Bayero Fullo ya bayyana cewa hanyar tattaunawa da masu ruwa da tsaki ne kawai hanyar magance matsalar taron da kasar nan ke fuskanta, amma ba da karfin bindiga ba.
Bala Bayero Fullo ya bayyana hakan ne a lokacin da yake ganawa da manema labarai a Kaduna, jim kadan bayan kammala wani taron bitar wayar wa da jama’a kai game da sanin dalilai da abin da ya kawo matsalolin da suke faruwa a Nijeriya, musamman a bangaren Fulani makiyaya.
Bala Bayero ya ci gaba da cewa, dole ne sai an kira al’umma waje daya, musamman Sarakuna da kuma jami’an tsaro domin lalubo me ke faruwa tun da farko kuma me ya haifar da wannan matsalar da nufin warware ta baki daya.
Ya kara da cewa, ana samun lokutan da ake kama masu mutane, wato Fulani, haka kawai a karbi abin hannunsu, ba su ji ba, ba su gani ba, kuma ba tare da sun yi wa kowa laifi ba, kuma a matsayinsu na ‘yan kasa, dole ya lalubo wannan da nufin magance lamarin, kuma a hukunta wadanda aka samu da laifi.
A game da dalilin da y asa suka kafa wannan kungiya ta matasan Fulani ta FASADAN kuwa, ya bayyana cewa domin wayar wa da Fulani baki daya kai a fannonin Ilimin addini da na Boko, “wanda hakika mun lura akwai bukatar hakan kwarai.
Ya ce, “mu Fulani masu son zaman lafiya ne kodayaushe a kowane irin lokaci, don haka muke fafutukar jama’a su fahimci hakan.”

SendShareTweetShare
Previous Post

Janar Kukasheka Ya Zama Sarkin Yakin Ketaren Katsina

Next Post

Babu Ranar Nadin Sabon Babban Sufeton ‘Yan Sanda, Cewar Fadar Shugaban Kasa

RelatedPosts

Alkalin Kotun Koli, Ngwuta, Ya Rasu A Abuja

Alkalin Kotun Koli, Ngwuta, Ya Rasu A Abuja

by Mustapha Abdullahi
14 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim Mai Shari’a Sylvester Ngwuta, alkalin kotun koli...

Tinubu Ya Bukaci Matasa Su Nisanci Bangar Siyasa

by Mustapha Abdullahi
20 hours ago
0

Daga Bello Hamza, Jagoran jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu, ya...

E Call

Shirin Kula Da Zirga-zirgar Manyan Motoci Na ‘E-Call’ Zai Kawo Karshen Cunkoso A Tashar Jiragen Ruwan Nijeriya -Hadiza Bala Usman

by Mustapha Abdullahi
21 hours ago
0

By Bello Hamza, An tabbatar wa masu hulda da tashoshin...

Next Post
Babu Ranar Nadin Sabon Babban Sufeton ‘Yan Sanda, Cewar Fadar Shugaban Kasa

Babu Ranar Nadin Sabon Babban Sufeton ‘Yan Sanda, Cewar Fadar Shugaban Kasa

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version