Tayar Da Yaki A Zamanin Nan Kauyanci Ne
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tayar Da Yaki A Zamanin Nan Kauyanci Ne

byCGTN Hausa and Sulaiman
4 weeks ago
Yaki

Yau saura kimanin shekaru 20 a cika karnin guda cif (shekaru 100) da karya lagon zaluncin amfani da yaki wajen mulkar mutane a doron kasa. Ba ina nufin ba a yaki a ko ina a cikin duniya ba a halin yanzu, har yanzu akwai wuraren da suke fama, ina nufin yaki mai gamewa irin wanda aka gwabza a yakin duniya na biyu wanda kasar Sin ta fafata da Japan, sauran sassan duniya suka fafata da Jamus da Italiya.

Duniya ta yi sabon zubi bayan cin nasarar yakin duniya na biyu, inda ya kai ga kafuwar Majalisar Dinkin Duniya domin samar da ’yanci da maslaha ga rayuwar bil’adama. An yi hakan ne da nufin bude hanyoyin samun ci gaba ta yadda duniya za ta yi dadin zama ba kawai ga mutane ba har da sauran halittun doron kasa. Wannan nasara ce babba, domin tana nuna al’ummar duniya sun dauki darasi daga kazamin yakin da ya salwantar da miliyoyin rayukan jama’a da kuma nuna wa duk wani mai mulkin kama-karya cewa zamanin cin karensa babu babbaka ya kare.

Sai dai kuma kash! A wannan karni na 21 da muke ciki, akwai masu kokarin sake maido da hannun agogo baya bisa barazanar sake maido da zamanin kauyanci na amfani da yaki domin “wai cimma muradu na kashin kai”. A makon da ya gabata, Amurka ta sake wa ma’aikatar tsaronta suna zuwa “Ma’aikatar Yaki” a karkashin wata dokar bangaren zartaswa wadda a karkashinta, kasar ta ce a shirye take ta tsunduma yaki don kare muradunta.

Ya kamata kasar ta fahimci cewa, mutanen zamanin nan suna da wayewa irin ta karnin da suke rayuwa a ciki. Yaki ba zai taba samar da nasara mai dorewa ba a zamanin nan. Kuma ita ce ma ya kamata ta fi kowa fahimtar hakan, domin ta gwabza a Afghanistan babu nasara, ta afka wa Iraki ba ta ci riba ba illa asara. Haka nan sauran wurare da ake ta nuna mata yatsa bisa tayar da fitina irin su Libiya har yau al’amura sun kasa daidaita yadda take muradi.

Ya kamata duk wata kasa da take nufin duniya da alheri a wannan zamanin, ta mayar da akalarta ga hanyoyin samun ci gaba da bunkasa cikin lumana. Karni na 21, karni ne da ilimi ya habaka sosai a duniya. Ta ko ina idan an duba za a ga yadda ake samun ci gaba a bangaren kimiyya da fasaha, da tattalin arziki da kuma wayewar kai da cudanyar jama’a. Duniya ta zamo dunkulalliya ta yadda wanda yake mahudar rana da mafadarta ba su yi nesa da juna ba.

Duk kasar da take son kawo wa al’ummarta ci gaba ta wayewar zamanin da muke ciki wajibi ne ta mayar da hankali a kan gwada basirar ilimin kirkiro da sabbin fasahohi na ci gaba wadda hatta sauran al’ummomi za su amfana, amma ba tayar da husuma da neman zubar da jini ko mai karfi ya danne mara karfi ba. Gudanar da gasa mai tsafta a ko wane fage na ci gaba halas ne, saboda hakan na samar da karin kuzarin ci gaba, amma ba komawa ga zamanin kauyanci na rayuwa tamkar ta namun daji ba! (Abdulrazaq Yahuza Jere)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?
Daga Birnin Sin

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
Next Post
Jagororin Tsaro Da Na Sojoji Daga Sama Da Kasashe 100 Za Su Halarci Taro Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Beijing

Jagororin Tsaro Da Na Sojoji Daga Sama Da Kasashe 100 Za Su Halarci Taro Na 12 Na Dandalin Xiangshan A Beijing

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version