Mustapha Ibrahim">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Tilastawa Kamfanoni Noma Zai Rage Tsadar Abinci, Ba Bude Iyakoki Ba – Munkaila Garba

by Mustapha Ibrahim
January 14, 2021
in LABARAI
2 min read
Munkaila Garba
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Tilasta wa kamfanoni masu sarrafa kayan amfani gona ne kawai zai rage tsadar amfani gona

Wannan bayanin ya fito ne daga bakin Alhaji Munkaila Garba, shugaban kunkiyar manoman Masara (MAAN) na kasa reshan Jihar Kano lokacin da ya ke ganawa da manema labarai kan batun bude iyakokin Nijeriya, ya ce a matsayinsu na manoma basa goyon bayan bode iyakokin Nijeriya domin abu ne da zai zama koma baya da cigaban noma da kamfanoni, kuma koma- baya ga tatalin arzikin kasa, domin a ce kasa bata dogaro da kanta sai da wata kasa wannan koma-baya ne don haka akwai bukatar a yi taka-cancan kuma a lura da kyau a yi abin da zai ciyar da kasarmu gaba ba baya ba a cewar shugaban MAAN na Kano.

samndaads

Har’ila yau ya ce kamfanoni masu sarrafa kayayakin amfanin gona kamar masara shinkafa dawa alkama, gyada, wake, da dai sauran kayan bukatu na yau da kullum da suke tsada ba don rufa iyakoki ba ne, a’a kamfanoni ne da suke bin Manoma a gonaki tun da danyar Kaka suna saye kayan amfani gona, wannan shi ne yake kawo tsada da karancin amfani gona.

Amma idan Gwamnatin Tarayya ta yi doka ta ce tilas ko wanne kamfani sai ya Noma kayan da zai sarafa ko da kashi 70 ko 50 cikin 100 ko kuma ya sa kunkiyoyi irin na mu su noma masa to yin haka ne zai sa a samu saukin kayan amfani gona a Nijeriya.

SendShareTweetShare
Previous Post

Cibiyoyin Da Aka Kama Da Satar Jarrabawar SSCE Sun Fuskanci Tsattsauran Hukunci

Next Post

PDP Na Cikin Jam’iyyun Da Suka Tsaya Takarkaru A Kananan Hukumomin Kano

RelatedPosts

Misali Daga Kebbi: Yadda Kananan Hukumomi Suka Shiga Uku A Nijeriya

Misali Daga Kebbi: Yadda Kananan Hukumomi Suka Shiga Uku A Nijeriya

by Mustapha Ibrahim
8 hours ago
0

Kamar dai yadda aka sani kananan hukumomi sune suka kasance...

Abubuwan Da Suka Biyo Bayan Canja Shugabannin Tsaron Nijeriya

’Yan Yankin Arewa Maso Gabas Sun Bayyana Ra’ayoyinsu Kan Sauke Shugabannin Tsaro

by Mustapha Ibrahim
8 hours ago
0

Biyo bayan sauke shugabannin tsaron Nijeriya tare da nada sababbi...

Ya Kashe Mata Da Yaro Da Shebur

by Mustapha Ibrahim
8 hours ago
0

A yau aka kama wani mutum mai shekaru 28, Chukwuemeka...

Next Post
PDP

PDP Na Cikin Jam'iyyun Da Suka Tsaya Takarkaru A Kananan Hukumomin Kano

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version