Tinubu Ya Himmatu Wajen Rage Raɗaɗin Da ‘Yan Nijeriya Ke Ciki, In Ji Minista
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Himmatu Wajen Rage Raɗaɗin Da ‘Yan Nijeriya Ke Ciki, In Ji Minista

bySulaiman
11 months ago
Tinubu

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya ce Shugaba Bola Tinubu ya ƙudiri aniyar rage raɗaɗin da ‘yan Nijeriya ke ciki.

 

Idris ya bayyana haka ne a ranar Lahadi a Kaduna a shirin ‘Hannu Da Yawa’ na Gidan Rediyon Tarayyar Nijeriya (FRCN), Sashen Hausa.

  • An Bukaci Amurka Da Ta Inganta Hadin Gwiwa Da Kasar Sin Kan AI
  • Katsewar Wutar Lantarki: Mun Yi Asarar Fiye Da Naira Biliyan 6 – KEDCO 

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN) ya ruwaito cewa ministan ya yi magana kan wahalar da aka samu sakamakon cire tallafin man fetur, kuma ya ce tallafin yana amfanar wasu tsirarun mutane ne kawai.

 

Ya ba da tabbacin cewa tattalin arzikin ƙasar nan zai daidaita, kuma babu wata gwamnati da za ta so a samu ci-baya a zamanin ta.

 

Idris ya jaddada cewa abin da ya kamata a gyara a ƙasar nan ba ya ta’allaƙa ne ga Majalisar Dokoki ta Ƙasa, wakilai da aka zaɓa ko kuma masu zartaswa na gwamnati kawai ba ne, amma har ga duk ‘yan Nijeriya ne.

 

Ya yi nuni da cewa a kwanakin baya Tinubu ya umurci ministoci da su rage kuɗin gudanar da mulki ta hanyar taƙaita yawan motocin su a lokacin da suke gudanar da ayyukan su da kuma yawan ma’aikatan su a lokacin tafiye-tafiye.

 

Idris ya ce, “Shugaba Tinubu yana nuna buƙatar a sauya daga yadda ake tafiyar da al’amura a Nijeriya.

 

“A duk lokacin da muka zauna taron Majalisar Zartaswa ta Tarayya (FEC), abin da Shugaban Ƙasa ke jaddadawa shi ne buƙatar a rage kashe kuɗaɗe da yawa waɗanda ba su zama dole ba wajen gudanar da mulki.

 

“Shugaba Tinubu har ma ya ba da sanarwa kan kuɗin tafiya da yawan ababen hawa. Ana iya ganin wannan a matsayin abu ƙanƙani, amma a zahiri yana da muhimmanci.”

 

Ministan ya ce ta fuskar noma, Tinubu ya ce an canja wa Ma’aikatar Noma da Raya Karkara suna zuwa Ma’aikatar Noma Da Samar Da Abinci ta yadda za a magance matsalolin noma ta ɓangarori daban-daban.

 

Haka zalika ya bayyana cewa Tinubu na magance matsalolin rashin tsaro kai-tsaye, inda ya ƙara da cewa tun kafin zuwan gwamnatin sa ne ake fuskantar matsalolin.

 

Idris ya ƙara da cewa har yanzu Gwamnatin Tarayya tana kan hanyar samar da dandamali da kuma tabbatar da jin daɗin jami’an tsaro domin inganta tsarin tsaron ƙasa.

 

Ya ƙara da cewa har yanzu Shugaban Ƙasa na neman shawarwari kan ba samar da ‘yan sandan jihohi.

 

Da yake ƙarin bayani, Idris ya ce ɗauke wutar lantarki da aka yi a sassan arewacin ƙasar nan kwanan nan ba wani shiri ne aka yi ba kamar yadda wasu suke cewa.

 

Ya nanata cewa babu wani shugaba da zai so da gangan al’ummar sa su kasance cikin halin rashin wutar lantarki da sauran matsaloli.

 

Ministan ya ƙara da cewa, “Shugaban Ƙasa yana bakin ƙoƙarin sa wajen ganin an samar da dauwamammiyar mafita kan matsalar lalacewar wuta a ƙasar nan.

 

“Haka nan ana gab da kammala aikin bututun iskar gas na AKK wanda zai taimaka wajen inganta masana’antu a Arewa.”

 

Idris ya buƙaci jama’a da su riƙa amfani da kafafen sadarwa na zamani wajen yaɗa labaran ƙasar nan ta hanyar da ta dace, yana kokawa da yadda ake yaɗa labaran ƙarya.

 

Ministan, yayin da ya yarda cewa lamari ne da ya shafi duniya, ya buƙaci yin amfani da kafafen ta hanya mai kyau.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Me Ya Faru Gwamna Abba Yusuf Ya Daina Ɗaukar Wayar Kwankwaso?

Me Ya Faru Gwamna Abba Yusuf Ya Daina Ɗaukar Wayar Kwankwaso?

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version