Tinubu Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Rikicin Manoma Da Makiyaya A Nijeriya
  • English
  • Business News
Tuesday, October 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Sha Alwashin Kawo Karshen Rikicin Manoma Da Makiyaya A Nijeriya

byAbubakar Abba
10 months ago
Tinubu

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya jaddada cewa; gwamnatinsa ta mayar da hankali wajen lalubo masu son zuba hannun jari a fannin kiwo a Nijeriya.

A cewar tasa, ta hakan ne za a iya kawo karshen yawan samun rikice-rikice a tsakanin Manoma da Makiyaya a fadin kasar tare da yakar yunwa da fatara da kuma kara habaka tattalin arzikin Nijeriyabaki-daya.

  • Nijeriya Ta Shirya Magance Matsalar Almajirai – Tinubu Ga Macron
  • Tinubu Zai Tafi Afirka Ta Kudu Daga Faransa

Tinubu ya bayyana haka ne, a cikin sanarwar da mai ba shi shawara na musamman a fannin sadarwa da tsare-tsare; Bayo Onanuga ya fitar a birnin de Janeiro,  na Kasar Brazil.

Sanarwar ta ce, shugaban ya yi wannan furuci ne a jawabinsa, bayan sanya hannu da wani kamfanin sarrafa Nama (JBS), a birnin Rio de Janeiro na kasar Brazil ya yi.

Kamfanin, ya kasance daya daga cikin manyan kamfanoni a duniya da ke sarrafa Nama.

A cewar tasa, abin da muka mayar da hankali yanzu a Nahiyar Afirka shi ne, lalubo mafita a kan rikice-rikicen Manoma da Makiyaya, musamman don rage asarar rayuka da dukiyoyi da kuma kara dawo da martabar kiwo.

Har ila yau, ya bukaci kamfanin ya yi amfani da wannan dama wajen sanya hannun jarin na kimanin dala biliyan 2.5, inda ya bai wa kamfanin tabbacin cewa; za a samar musu da kyakkyawan yanayi na yin kasuwanci.

Shi kuwa, Ministan Ma’aikatar Bunkasa Kiwon Dabbobi; Idi Muhktar Mahia, wanda ya jagoranci wata tawaga da Tinubu ya tura zuwa taron kafin ya isa kasar ta Brazil, a jawabin da ministan ya yi wa Tinubu ya sheda masa cewa, ya kai ziyara ga wasu manyan kamfanoni a Brazil; domin duba yadda suke gudanar da ayyukansu da kayan aiki na zamani kan sarrafa Nama.

Kamfanin na JBS S.A, na sarrafa Shanu 33,000 tare da tsintsaye sama da miliyan takwas, wanda ya sanar da cewa; yana da kyau Nijeriya ta yi hadaka da su.

Idi ya kara da cewa, kamfanin na da ma’aikata sama da 200,000 da suka fito daga sama da kasashe 50, ciki har da Kasar Amurka Kanada, Mexico da kuma Saudiya.

Haka zalika, shugaban kamfanin Wesley Batista; ya bayyana jin dadinsa kan yunkurin wannan hadaka, inda ya sanar da cewa; mun ji dadi da za mu yi aiki da Nijeriya, domin kara habaka fannin kiwon kasar.

Haka nan, Batista ya bayar da tabbacin cewa; nan ba da jimawa ba ake sa ran, kamfanin na  JBS; zai fara gudanar da ayyukansa a Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci
Labarai

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Next Post
Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati 2024: Shugaban Kwastam, Alh. Bashir Adewale Adeniyi

Gwarzon Ma'aikacin Gwamnati 2024: Shugaban Kwastam, Alh. Bashir Adewale Adeniyi

LABARAI MASU NASABA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Na Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Korea Ta Arewa

Firaministan Sin Zai Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Na Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Korea Ta Arewa

October 7, 2025
Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version