Trump Da Harris Sun Caccaki Juna A Muhawara
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Trump Da Harris Sun Caccaki Juna A Muhawara

byRabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Trump

Tsohon shugaban Amurka kuma dan takarar jamiyyar Republican a zaben kasar mai zuwa Donald Trump da mataimakiyar shugaban kasar kuma ‘yar takarar jamiyyar Democrat, Kamala Harris sun gwabza a kan batun tattalin arziki da ‘yancin zubar da ciki da kuma manufar shige da fice a muhawararsu ta farko a kan zaben shugaban kasar da za a yi a watan Nuwamba.

Muhawarar wadda sau da dama ta kan karkata ga suka da cin dunduniyar juna, ta tabo bangarori da dama da suka kama daga abubuwan da suka jibinci batun manufofi da waje da tattalin arziki.

  • Sakon Da Aka Isar Game Da Yanayin Tekun Kudancin Kasar Sin Daga Wasu Taruka Uku
  • Kotu Ta Dakatar Da Yunkurin Aminu Ado Bayero Na Gyaran Fadar Nassarawa

Muhawarar wadda ta kasance ta farko a tsakaninsu kasancewar ba su taba haduwa gaba da gaba ba ta fara ne da ban mamaki, inda Kamala Harris ta tunkari Donald Trump ta yi musabaha da shi a abin da za a ce musabaha ta farko a wata muhawar ta masu neman shugaban kasa tun 2016.

Muhawara dai ta kasance mai muhimmanci musamman ga ita Kamala Harris, wadda kuriar jin ra’ayin jama’a ta nuna cewa sama da kashi daya bisa hudu na masu zabe ke ganin ba su da masaniya sosai a kanta.

‘Yan takarar biyu sun bude muhawara ne da ta hanyar mayar da hankali kan batun tattalin arziki, bangaren da kur’iar jin ra’ayin jama’a ta nuna Trump ya fi dama.

Harris ta soki aniyar Trump ta sanya haraji mai yawa a kan kayayyakin waje, wanda shiri ne da ta kwatanta da haraji a kan masu matsakaicin samu, inda ta tallata shirinta na rage haraji ga iyalai da masu kananan harkokin kasuwanci.

Haka kuma Harris ta soki Trump da janyo rashin akin yi a Amurka a lokacin yana shugaban kasa daga 2017 zuwa 2021.

Sannan shi kuma ya soke ta a kan yawan tashin farashin kaya da ayyuka da ya ce an rika samu a lokacin mulkin Biden, kodayake ya rika kara gishiri a kan yadda aka samu karuwar farashin

Sannan kuma nan da nan ya karkata a kan babban batun da ya fi sanyawa a gaba na shige da fice, inda ya yi ikirari ba tare da wata sheda ba cewa bakin haure sun rika shiga Amurka daga iyakarta ta kudu da Medico.

‘Yar takarar ta Democrat ta gabatar da jawabi mai tsawo na suka a kan ‘yancin zubar da cikin da ake magana kan yadda take ganin an danne wa mata ‘yancinsu na samun kulawar gaggawa a harkar lafiya, da kuma yadda matan suka rasa damar zubar da ciki saboda dokoki na jihohi da suka samu gindin zama tun bayan da kotun kolin kasar ta kawar da damar da jihohi ke da ita a kan hakan a 2022.

Hukuncin da ta danganta da alkalai uku na kotun da Trump ya nada.

A kan manufofin waje Mista Trump ya ki ya masa cewa ko yana ganin ya kamata Ukraine ta yi nasara a yaki da Rasha, yayin da ya zargi Harris da tsanar Isra’ila.

A kan batun na Ukraine Harris tana nuna goyon baya ne ga wadanda ta kira kawayen Amurka, yayin da ta jadda ‘yancin Isra’ila na kare kanta da tabbatar da tsaronta, to amma tana ganin hanyar lafiya ita ce samar da kasashe biyu na Isra’ila da kuma Falasdinawa da ta ce sun cancanci samun tasu kasar cikin ‘yanci da walwala.

Mis Hariis ta soki Trump a kan samun sa da kotu ta yi da laifi a kan shari’arsa ta bayar da kudi na toshiyar baki ga fitaccciyar mai fim din batsa da ya yi mu’amulla da ita da sauran laifuka da aka same shi da su.

Trump ya musanta aikata wani laifi a nan inda ya sake zargin Harris da jam’iyyarta ta Democrat da kulla masa sharri a kan dukkanin wadannan laifuka ba tare da sheda ba.

Haka kuma Trump ya sake ikirarinsa na cewa zaben 2020 ya fadi ne saboda magudi da ya ce an yi masa.

Yanzu dai mako takwas ya rage a yi zaben.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto
Kasashen Ketare

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?
Kasashen Ketare

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?
Kasashen Ketare

Wadanne Kasashen Afirka Ne Ba Sa Goyon Bayan Kafa Kasar Falasdinawa?

September 28, 2025
Next Post
Zaben Kananan Hukumomi: A Magance Maimaita Magudi A Jihar Kaduna

Zaben Kananan Hukumomi: A Magance Maimaita Magudi A Jihar Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version