Trump Ya Bayyana Dalilin Rufe Gidan Rediyon Muryar Amurka
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Trump Ya Bayyana Dalilin Rufe Gidan Rediyon Muryar Amurka

byRabi'u Ali Indabawa and Sulaiman
7 months ago
Trump

Shugaban Amurka Donald Trump ya ba da umarnin rufe Gidan Rediyon Muryar Amurka (VOA) da ke samun tallafin gwamnati, bisa zarginsa da yada labaran son zuciya.
Wani babban jami’in fadar White House ya nakalto a kafar yada labara ta FOd News cewa “Muryar Amurka ba ta bin tafarkin Amurka tsawon shekaru.

A ranar Juma’ar da ta gabata ce Trump ya rattaba hannu kan wata doka da ta rushe wasu ma’aikatun gwamnati guda bakwai da suka hada da Hukumar Kula da Kafofin Yada Labarai ta Amurka, ciki har da Muryar Amurka da kuma Rediyon Free Europe/Radio Liberty.

  • Sin Ta Ba Da Jawabi A Kwamitin Kare Hakkin Bil’adama Na MDD A Madadin Kungiyar Abokantaka Ta Inganta Hakkin Bil’adama
  • El-Rufa’i Ya Yi Kadan Ya Sa Mu Bar Jam’iyyar PDP – Sule Lamido

“Za a kawar da abubuwan da ba na doka ba da ayyuka na hukumomin gwamnati domin su zama sun yi daidai da dokar da ta dace, kuma irin wadannan kungiyoyi za su rage ayyukansu domin su kasance suna aiki kamar yadda doka ta bukata,” in ji umarnin zartarwar.

Hukumar Kula da Kafofin Yada Labarai ta Amurka (USAGM) da babban mai ba ta shawara, Kari Lake, sun ce hukumar “ba za a iya warware matsaloli ba.”

An ba da rahoton cewa, ma’aikatan Muryar Amurka sun sami sanarwar sauye-sauyen ta hanyar imel daga Crystal Thomas, darektan hulda da jama’a na USAGM.

An kuma sanar da ma’aikata masu zaman kansu da ‘yan kwangila na kasa da kasa kan dakatar da ba da tallafi. A lokaci guda kuma, an daina ba da tallafi na tarayya ga gidajen Rediyon ‘Free Asia da Rediyo Free Europe/Radio Liberty’.

Daraktan Muryar Amurka, Mike Abramowitz, ya ce shi da kusan dukkan ma’aikatansa 1,300 an ba su hutun biyan albashi biyo bayan umarnin.

Har ila yau, umarnin zartarwa ya shafi wasu hukumomi, ciki har da Ma’aikatar Sasanci da Shiga Tsakani ta Tarayya; Hukumar Yada Labarai ta Duniya ta Amurka; Cibiyar Nazarin Duniya ta Woodrow Wilson, Cibiyar Smithsonian; Cibiyar Gidan Tarihi da Ayyukan Laburare; Majalisar Sadarwar Amurka; Asusun Ci gaban Al’umma na Cibiyoyin Kudi; da Hukumar Bunkasa kananan Kasuwanci.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Next Post
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili

Wike Ya Kwace Filaye 4,794 A Abuja Saboda Rashin Biyan Kudin Ka’ida

LABARAI MASU NASABA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version