Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Trump Ya Gargadi Kasashen Turai Kan Mayakan IS

by
3 years ago
in KASASHEN WAJE
1 min read
Trump Ya Gargadi Kasashen Turai Kan Mayakan IS
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Yi Ruwan Tiyagas Kan Musulmai A Sahun Sallar Idi A Ethiopia

Mutum 8 Sun Mutu, 43 Sun Jikkata A Wani Mummunan Hatsarin Mota A Saudiyya

Shugaban Amurka Donald Trump ya bukaci kasashen Turai da su karbi karuruwan mayakan ISIS domin yi musu shari’a bayan dakarun SDF sun cafke su a Syria, yayin da ya yi barazanar sakin su muddin kasashen na Turai suka yi watsi da bukatarsa.
A wani sako da ya aika a shafinsa na Twitter, shugaba Trump ya ce, Amurka ba ta fatan zura ido kan mayakan na ISIS har su mamaye nahiyar Turai, yana mai cewa, sun yi aiki tukuru tare da kashe makuden kudade, a don haka lokaci ya yi da wasu kasashen za su hubbasa wajen gudanar da aikin da bai fi karfin su ba.
A cewar Trump, Amurka na bukatar kasashen Birtaniya da Faransa da Jamus da sauran kasashen Turai da su karbi mayakan na ISIS da yawansu ya zarce 800, in da ya yi barazanar cewa, matsin lamba ka iya tilasta wa Amurkan sakin wadanda mayakan, yayin da a gefe guda, jami’an gwamnatin Trump suka bayyana fargabarsu game da hadarin da ke tattare da sakin mayakan masu ikirarin jihadi.
Sama da makwanni biyu kenan da gwamnatin Trump ke bukatar wadannan kasashe da su karbi mayakan ‘yan asalin nahiyar Turai, kuma Amurka ta ce, a shirye take ta tasa keyarsu.
Kalaman Mr. Trump sun karfafa tsokacin shugaban Hukumar Leken Asirin Birtaniya wanda ya gargadi cewa, Kungiyar mayakan ISIS na sake kintsa kanta domin kaddamar da wasu sabbin hare-hare a kasashen Turai duk da cewa, dakarun soji sun ci galabar su a Syria.
A cikin watan Disamban da ya gabata ne, Trump ya girgiza manyan aminan Amurka bayan ya sanar da matakinsa na janye kimanin sojojin Amurka dubu 2 daga Syria bisa ikirarinsa na cin galabar mayakan na ISIS.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Saudiya Za Ta Zuba Jarin Dala Biliyan 20 A Pakistan

Next Post

May Ta Sake Shan Kaye A Majalisar Birtaniya Kan Brexit

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Yi Ruwan Tiyagas Kan Musulmai A Sahun Sallar Idi A Ethiopia

Jami’an Tsaro Sun Yi Ruwan Tiyagas Kan Musulmai A Sahun Sallar Idi A Ethiopia

by Khalid Idris Doya
2 weeks ago
0

...

Mutum 8 Sun Mutu, 43 Sun Jikkata A Wani Mummunan Hatsarin Mota A Saudiyya

Mutum 8 Sun Mutu, 43 Sun Jikkata A Wani Mummunan Hatsarin Mota A Saudiyya

by
3 weeks ago
0

...

Jirgin Ruwan Yakin Rasha Ya Dulmiye Cikin Tekun Black Sea

Jirgin Ruwan Yakin Rasha Ya Dulmiye Cikin Tekun Black Sea

by
1 month ago
0

...

Isra’ilawa Sun Zargi Falasdinawa Da Kai Farmaki Kan Kabarin Annabi Yusuf

Isra’ilawa Sun Zargi Falasdinawa Da Kai Farmaki Kan Kabarin Annabi Yusuf

by Muhammad Bashir
1 month ago
0

...

Next Post

May Ta Sake Shan Kaye A Majalisar Birtaniya Kan Brexit

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: