Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Tsadar

Kamuwa da rashin lafiya a Nijeriya ya zama kalubalen da za a iya cewa ruwan dare, amma samun jinya da magani kuma sai su zama babban kakanikayi sakamakon tsadar magunguna da ‘yan Nijeriya da dama ba su iya saye.

Tsadar magungunan musamman wadanda ake amfani da su yau da gobe irinsu rigakafi, maganin suga, ciwon kai, mura, maleriya da sauran cutukan da jama’a ke yawan fama da su na yau da kullum, abun da kawai majinyatan ke iyawa shi ne tururuwa zuwa asibitoci domin neman waraka.

  • Gwamnatin Zamfara Zata Raba Dabbobi Kyauta Ga Mata
  • Gwamnatin Zamfara Zata Raba Dabbobi Kyauta Ga Mata

Tsadar kayan magunguna babban barazana ne da ke fuskantar yawaitan zuwa asibitoci domin neman jinya, lamarin da ke neman a gaggauta daukan matakin shawo kansa domin kauce wa yawaitar mace-macen majinyata sakamakon rashin kudi ko kasa sayen magunguna.

Majinyata da dama sun nuna halin da suke ciki na mawuyacin yanayi musamman wadanda suke fama da karamin karfi kuma ba su cikin shirin inshuran kiwon lafiya, kamar wata uwa, Idowu Akinyemi wacce take fama da ciwon suga, ta shiga mamaki lokacin da ta je sayen magungunanta bisa gano yadda maganin ya yi tashin gwauron zabi farad daya.

“Lokacin da na sayi maganina na karshe shi ne, naira dubu 3,000, amma yanzu maganin da na je shagon sayar da magunguna ya kai naira 5,000,” Idowu ta nuna damuwarta kan tashin magungunan.

Dokun Bolarinwa, mai fama da ciwon hawan jini, ya ce, yana kan magani da jinya a kowani lokaci, amma tsadar magungunan sannu a hankali ya sanya shi kauce wa ka’ida da dokokin da likita ta dora shi a kai.

“Ni tsohon ma’aikaci ne ba na da wata hanyar samun kudi a kowani lokaci. ‘Yan shekaru, ina ta fama da jinyar da ke damuna tare da gudunmawar ahlina, amma a ‘yan kwanakin nan gaskiya lamuran sun mana wuya. Na koma tsallake ranakun shan magani domin ba mu iya sayen maganin a kowani lokaci.”

Ade Ogun, wanda ya sayo maganinsa, sai dai ransa a bace cikin damuwa yayin da ya gano cewa maganin da yake amfani da shi ya tashi, “Na sayi maganina a baya kan kudi naira 500, amma da na koma ya tashi da kaso 100, na yi matukar mamakin tashin maganin har haka,” Ade ya shaida.

Funmi Olaoye, matar aure ce wacce uwa ce kuma, da take jinyar danta mai fama da ciwon Asma, ta ce, “Yarona yana matukar bukatar kulawar magani kan ciwon asma da yake fama da shi, amma ba na iya sayen rashin maganin da ya dace na saya saboda tsada,” ta koka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci
Labarai

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Next Post
alkawari

Kyan Alkawari Cikawa

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version