Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home KASASHEN WAJE

Tsarin Mulkin Togo: ‘Yan Adawa Sun Jajirce

by Tayo Adelaja
September 13, 2017
in KASASHEN WAJE
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Shugabanin adawa a Togo sun ce, ba abin da su ke bukata face sauya kundin tsarin mulkin kasar, sabanin sauye sauyen da gwamnati ta yi alkawarin samarwa. Hakan dai na zuwa ne bayan zanga zangar kin jinin gwamnatin da ‘yan adawar suka rika gudanarwa a baya-bayan nan, wadda ta samu halartar dubban ’yan adawa a manyan biranen kasar.

Eric Dupuy, kakakin hadakar jamíyyun adawar 5 Cap 2015 – kungiyar da ta jagoranci zanga-zangar ranakun Laraba da Alhamis, domin ganin a siyasance an samar da sauyin gwamnati a Togo, ya danganta sauye sauyen da gwamnatin ta ce za ta samar a matsayin jan kafa, inda ya ce ba shi ne abin da su ke bukata ba.

Shugaban kasar ta Togo, Faure Gnassingbé, ya dare kan karagar shugabancin kasar shekaru 12 da suka gabata bayan mutuwar mahaifinsa, Gnassingbé Eyadéma.

Mahaifinsa janar Eyadéma ya mulki ’yar karamar kasar ta Togo da ke yankin Yammacin nahiyar Afrika na tsawon shekaru 40 sakamakon wani juyin mulkin soja da ya yi wa gwamnatin farar hula.

Yau shekaru 10 ke nan ’yan adawar ta Togo ke bukatar ganin an sake fasalta kundin tsarin mulkin 2002 da aka kwaskwarimance, musaman ta bagaren sake mai do da dokar takaita wa’ádin shugabancin kasa shekaru 10 a wa’ádin shekaru biyar-biyar sau 2 babu kari.

A wata sanarwar bayan taron majalisar ministoci ta marecen ranar Talatar da ta gabata, gwamnati ta yi wani yinkuri da ake ganin sassauci ne akan matsayinta, inda ta bayyana aniyar samar da gyare gyare ga kundin tsarin mulkin musaman ta bangaren takaita wa’ádin shugabanci da kuma tsarin zabe da ke kunshe a kundin.

SendShareTweetShare
Previous Post

Faransa Ta Bukaci Chadi Ta Gudanar Da Zaben ‘Yan Majalisu

Next Post

Amurka Za Ta Dandana Kudarta —Koriya Ta Arewa

RelatedPosts

Mijin Sarauniya Elizabeth Ta Ingila Ya Mutu

Mijin Sarauniya Elizabeth Ta Ingila Ya Mutu

by Muhammad
1 week ago
0

Rahotanni daga Fadar Buckingham ta kasar Ingila sun tabbatar da...

Nijer

Matan Nijer Sun Dage Kan ‘Yancinsu Bayan Kotu Ta Sako Wasu Shugabanninsu

by Muhammad
4 weeks ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Hukumomi a jamhuriyar Nijer sun sako...

Magufuli

Muhimman Abubuwa Goma Game Da Tsohon Shugaban Tanzaniya John Magufuli

by Muhammad
4 weeks ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Al'ummar kasar Tanzania suna zaman makokin...

Next Post

Amurka Za Ta Dandana Kudarta —Koriya Ta Arewa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version