Nasir S Gwangwazo">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Tsaro: Buhari Zai Fede Biri Har Wutsiya A Bainar Jama’a Ranar Alhamis

by Nasir S Gwangwazo
December 8, 2020
in RAHOTANNI
2 min read
Fede Biri Har Wutsiya

PRESIDENT BUHARI IN A VIRTUAL OPENING OF CHIEF OF ARMY STAFF ANNUAL CONFERENCE .00A. President Muhammadu Buhari during a virtual opening of the Chief of Staff Annual Conference at the Council Chambers, ABUJA. PHOTO; SUNDAY AGHAEZE.DEC 7 2020

WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari zai fede biri a bainar jama’a kan tabarbarewar harkokin tsaro da ke addabar kasar, musamman ma Arewacin Nijeriya ranar Alhamis mai zuwa lokacin da zai bayyana a gaban Majalisar Wakilai Kasa.

Majiyar Fadar Shugaban Kasa ta shaida wa LEADERSHIP A YAU cewa, hakan ya biyo bayan amincewar da Shugaba Buhari ya yi ne na gabata a gaban majalisar sakamakon gayyatar da su ka yi ma sa bayan da a ka kai mummunan harin kisan kiyashin Zabarmari a Karamar Hukumar Jere da ke Jihar Borno, inda a ka kashe wasu manoma da masunta guda 43.

samndaads

Majiyar ta ce, shugaban zai mayar da hankali ne kan harkokin tsaro dungurum a fadin kasar bakidaya, musamman ma Arewa.

Idan dai za a iya tunawa, a makon jiya ne Kakakin Majalisar Wakilan Nijeriya, Rt. Hon. Femi Gbajiamila, ya kai sakon kiranyen ’yan majalisar wakilan ga Shugaba Buhari, inda kuma bayan fitowarsa daga ganawar tasu ya shaida wa manema labarai cewa, shugaban ya amince da kiran da su ka yi ma sa, kamar yadda Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya ya ba su iko.

Kisan kiyashin ya haifar da kiraye-kirayen neman sauke shugabannin tsaron kasar da ma shi kansa Shugaba Buhari. Ita kanta Majalisar Dattawan Nijeriya ta maimaita kiranta ga Shugaban Kasar da ya sauke shugabannin tsaron a karo na uku.

Ita kuwa Majalisar Wakilai ta nemi Shugaban Kasar ya gurfana a gabanta ne bayan wata tattaunawa mai zafi a tsakanin mambobinta, inda daga bisani a ka amince da kudirin kiran shugaban kasar bayan shugabannin majalisar sun yi ganawar sirri, don saisaita al’amura.

Jim kadan bayan amincewa da a kira Shugaba Buharin, don yin bayani kan tabarbarewar al’amuran tsarin ne, sai Kakakin Majalisar ya bazama Fadar Shugaban Kasa, don mika goron gayyatar.

Jim kadan bayan fitowarsa ne ya shaida wa mafarauta labaran fadar cewa, “mun amince da ranar da zai bayyana gaban majalisa, don yi ma ta bayanin halin da a ke ciki. Mun tsayar da rana, amma za mu sanar da ku nan gaba kadan,” in ji shi.

Sai a yanzu ne wata majiyar Fadar Shugaban kasar ta shaida wa LEADERSHIP A YAU cewa, an tsayar da ranar Alhamis mai zuwa, 10 ga Nuwamba, 2020, a matsayin ranar da Shugaban Kasar zai gabata a gaban majalisar.

Shi kuwa Malam Garba Shehu, mai magana da yawu Shugaba Buhari, ya shaida cewa, Shugaban Kasar zai yi jawabi ne ga majalisun dokokin kasar guda biyu, ba wai Majalisar Wakilai kadai ba, wato har da Majalisar Dattawa kenan.

SendShareTweetShare
Previous Post

Sanata Lawan Ya Lashe Kyautar Shugabanci Ta Zik Ta 2019

Next Post

Limamin Masallacin Juma’ar Gesse Ya Tsine Wa Wanda Ya Zuba Ruwan Kashi A Masallaci

RelatedPosts

Ta’aziyar Rasuwar Sam Nda Isaiah

Sam Nda-Isaiah Ya Rasu Lokacin Da Ake Tsananin Bukatar Gudunmawarsa – Jami’ar Jos

by Nasir S Gwangwazo
2 days ago
0

Shugabannin jami’ar Jos sun bayyana rashin jin dadinsu dangane da...

Kasuwar Mile 12

Kwamitin Da Shugaban Kasuwar Mile 12 Ya Nada Na Cigaba Da Jajanta Wa Manoman Arewacin Nijeriya

by Nasir S Gwangwazo
2 days ago
0

Sabon kwamitin da Babban Shugaban kasuwar mile 12 Intanashinal market...

Sojoji Sun Farmaki Mahakar Ma’adanai A Zamfara, Sun Cafke ‘Yan Bindiga 150

Ranar Mazan Jiya: Babu Wani Abin Murna Ga Tabarabrewar Tsaro – Dattawa Ga Buhari

by Nasir S Gwangwazo
2 days ago
0

Dattawan Nijeriya a karkashin inuwar gamayyar kungiyar wato (COPANE), sun...

Next Post
Masallacin Juma'ar Gesse

Limamin Masallacin Juma'ar Gesse Ya Tsine Wa Wanda Ya Zuba Ruwan Kashi A Masallaci

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version