Rabiu Ali Indabawa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home KASUWANCI

Tsoffin Jami’an Gwamnati Na Fargaba Kan Kwangilar Da Ta Jefa Najeriya Bashi

by Rabiu Ali Indabawa
October 3, 2019
in KASUWANCI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

  Tsoffin jami’an gwamnati da kuma wasun da suke aiki yanzu na cikin zullumi da tashin hankula – A ko yaushe za a iya bukatar tattaunawa ko gurfanar da wadanda ke da hannu a kwangilar P&ID da ta jefa Najeriya a bashin $9.6bn – Gwamnatin tarayya na kokarin ganin a kara duban shari’ar inda majalisar wakilai da hukumar yaki da rashawa ta EFCC ke kokarin zakulo masu hannu a aika-aikar A halin yanzu, jami’an gwamnati da tsoffin jami’an na cikim tsoron binciken hukuncin bashin kamfanin P&ID da aka yankewa Najeriya. Gwamnatin tarayya ta garzaya kotun turai don kawo maslaha akan bashin. ‘Yan majalisar wakilai da hukumar yaki da rashawa ta EFCC na bincikar yadda abin ya kasance.

An gano cewa, masu bincike na ta zakulo bayanai akan kwangilar. “Masu bincike a kullum na cikin gano wadanda aka hada kai dasu wajen take dokokin cikin gida da na kasashen duniya akan kwangilar. Za a iya amfani da binciken wajen gurfanar da wadanda suka karya dokar har ta kai ga wannan badakalar,” in ji wata majiya mai karfi.

samndaads

An gano cewa kuma, hukumar yaki da rashawa ta shirya don gurfanar da tsoffin ma’aikatan gwamnatin tarayya na lokacin. Tsohon mataimaki na musamman ga shugaban kasa ya sanar da jaridar The Nation cewa, zargin da hukumar rashawa ke wa wasu jami’an gwamnati zai iya bankado sirrika da yawa. Ya ce: “Dukkanmu jira muke mu ga abinda zai faru. Matsalar P&ID za ta iya zama wata dama da wasu mutane ke jira don kai wasunmu kasa.

Lokacin magana bai yi ba amma zan iya sanar da ku cewa duk a tsorace muke.” Wata majiya kuma, tsohon mataimaki na musamman ga wani minista ya ce: “Shari’a da bincike akan P&ID ta isa ta sanya mutane da dama cikin tashin hankali. An gano sunayen masu hannu a ciki kuma bincike na cigaba. Kowa a tsorace yake. Mun yi aiki ne a wancan lokacin da umarni da aka bamu.” An gano cewa, hukumar EFCC na cigaba da gano jami’an gwamnati da ke da hannu dumu-dumu cikin taimakon kamfanin don cutar da kasar. Majiya mai karfi ta ce, za a cigaba da gayyatar mutane don amsa tambayoyi saboda hukumar da kara gano wasu tsoffin jami’an gwamnatin da ke da hannu a ciki.

SendShareTweetShare
Previous Post

Yanar Gizo Na Kara Habaka Kasuwancin Zamani

Next Post

Yakamata Gwamnatin Tarayya Ta Kakaba Haraji Kan Kangayen Gidaje, Cewar UN

RelatedPosts

Sugar

Alakar Dake Tsakanin Sukari Ca Ciwon Suga

by Rabiu Ali Indabawa
3 weeks ago
0

Da yawa a yankin kasashen nahiyar Afirka ana ganin sukari...

A Na Cigaba Da Zaman Doya Da Man Ja Tsakanin Majalisa Da Shugaba Trump

Ba Da Mugun Nufi Shugaba Buhari Ya Garkame Iyakoki Ba – Ministar Kudi

by Rabiu Ali Indabawa
1 year ago
0

Ministar kudi da tsaretsare, Uwargida Zainab Ahmed Shamsuna, ta sanar...

Gwamnatin Tarraya Ta Kebe Biliyan N2.6 Don Aikin Tashar Mambilla A 2020

by Rabiu Ali Indabawa
1 year ago
0

Sama da shekaru arba’in da suka shude kenan da bada...

Next Post

Yakamata Gwamnatin Tarayya Ta Kakaba Haraji Kan Kangayen Gidaje, Cewar UN

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version