Tsohon Dan Majalisar Tarayya, Ibrahim IMBA Ya Sauya Sheka Zuwa APC
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tsohon Dan Majalisar Tarayya, Ibrahim IMBA Ya Sauya Sheka Zuwa APC

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Dan majalisa

Tsohon dan majalisar wakilai ta tarayya kuma dan takarar Sanatan Bauchi ta Arewa a karkashin jam’iyar Social Democratic Party (SDP) a zaben 2023, Hon. Ibrahim Mohammed Baba IMBA ya sauya sheka zuwa jam’iyyar APC.

IMBA wanda ya shelanta komawa jam’iyyar a ranar Juma’a kuma ya samu tarba daga wajen shugaban jam’iyyar APC a gundumar Nasarawa Bakin Kasuwa a karamar hukumar Katagum, Adamu Abubakar da suka karbe shi a ofishin jam’iyyar da ke gundumar.

  • Hatsarin Mota Ya Ci Rayukan Mutum 8, Ya Jikkata 7 A Bauchi
  • Gwamnan Bauchi Ya Nada Sarkin Ningi A Matsayin Amirul Hajj Na 2023

IMBA ya kasance dan majalisar wakilai ta tarayya mai wakiltar mazabar Katagum tsakanin shekarar 2015 zuwa 2019 da ya samu nasarar tafiya majalisar a karkashin jam’iyyar APC daga bisani kuma ya fice daga jam’iyyar bayan wasu ‘yan matsaloli.

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida kan dalilinsa na sake dawowa cikin jam’iyyar APC, Ibrahim Baba IMBA ya ce sun dawo tare da magoya bayansa ne domin gina jam’iyyar da sake farfado da ita, kana ya na mai cewa dukkanin matakan da suka dace na gyara jam’iyyar za su yi.

Ya ce, “Babban dalilina shi ne muna son mu dawo mu sake gina ita jam’iyyar saboda ta dawo hayyacinta. Kamar a 2015 an fusata mutane da yawa, mutane sun yi fushi sosai a jihar Bauchi saboda wasu dalilai, hakan ya sanya wadansunmu suka fita, wasu sun dawo wasu kuma har yanzu ba su dawo ba, wasu kuma har yanzu din su na cikin jam’iyyar amma ba su taimakonta.

“Wannan dalilin ya sanya muka ce bar mu dawo domin a zo a gyara tsarin.”

Ya ce su na sane har yanzu har gobe hankalin al’ummar jihar Bauchi na kan jam’iyyar APC, “Dawowarmu din zai taimaka wajen shawo kan matsalolin da ake fama da su musamman rikicin cikin gidan nan. Idan muka samu zo muka zauna muka samu wadanda lamarin ya shafa tun da mu din ma mun fita amma mun san ciwon da ya sa muka fita, don haka da yardar Allah za mu samu masu ruwa da tsaki a zo a ga an zauna da su domin tabbatar jam’iyyar ta sake samun nasara a gaba kuma al’umma su mori nasarar da aka samu.”

A cewarsa, babu abun da tattaunawa ba zai gyara shi ba, don haka ya ce rikicin cikin gida da ke APC za su yi kokarin magance shi nan ba da jimawa ba, “Duk lokacin da mutane suka zauna suka fitar da abubuwan da suke ganin ya dace a yi da wadanda suke ganin bai dace a yi ba, ta haka za a samu mafita kan matsaloli sosai.”

IMBA ya kuma shaida cewar sai da ya tuntubi magoya bayansa da masu ruwa da tsaki kafin daukan wannan matakin inda suka mara masa baya tare da sake biyo shi suka dawo APC.

“Na tuntubi magoya bayana sosai kafin muka dauki wannan matakin, kuma tun lokacin da muka koma ita wancan jam’iyyar har muka yi takara magoya bayana da dama basu fito sun shiga wancan jam’iyyar ba, sun dai je sun mara mana baya ne a zabe wanda kowa ya ga yadda zaben ya kasance musamman a karamar hukumata ta Katagum, wannan dalilin ya sanya dole mu sauraresu mu dawo mu kula da wadanda suka fi bukatar mu yi mu’alamar siyasa da su.”

Shi ma a nasa bangaren, shugaban jam’iyyar APC a gundumar Nasarawa Bakin Kasuwa a karamar hukumar Katagum, Adamu Abubakar, ya nuna jin dadinsu bisa dawowar IMBA cikin jam’iyyar, yana mai cewa tabbas jam’iyyar cike take da farin cikin samun irinsa lura da irin tasirin da ke da shi a siyasance.

Ya kuma bada tabbacin cewa a matsayinsa na mai fada a ji, zai kawo cigaba musamman wajen tabbatar da hadin kai da cigaban jam’iyyar, sai ya masa lale da dawowa jam’iyyarsa ta asali.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas
Labarai

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas

October 2, 2025
Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni A Kwara

September 28, 2025
Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas
Siyasa

Tinubu Zai Gana Da Manyan Ƴan Kasuwa, Zai Ƙaddamar Da Muhimman Aiyuka A Legas

September 27, 2025
Next Post
Labarin Dutsen Nyiragongo Mai Dauke Da Tsawa

Labarin Dutsen Nyiragongo Mai Dauke Da Tsawa

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version