Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home TATTALIN ARZIKI

Tun A 2016 Tattalin Arzikin Nijeriya Ya Rage Habaka – Minista

by Muhammad
March 24, 2021
in TATTALIN ARZIKI
1 min read
Minista
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Mahdi M. Muhammad,

Karamin Minista na Kasafin Kudi da Tsare-tsaren Kasa, Prince Clem Agba, ya bayyana cewa, ci gaban tattalin arzikin Nijeriya ya yi matukar raguwa a cikin shekaru biyar da suka gabata.

Ya bayyana hakan ne a ranar Litinin lokacin da yake gabatar da matsakaicin tsarin ci gaban kasa (MTNDP) na shekarar 2021 zuwa 2025, a wani taron jin ra’ayoyin jama’a da kwamitin majalisar wakilai kan tsara kasa da ci gaban tattalin arziki ta gudanar.

Ya cigaba da cewa, tattalin arzikin kasar ya bunkasa da matsakaicin kasa da kashi biyu cikin dari a lokacin.

Ministan ya ce, rashin ci gaban tattalin arziki mai inganci, kasar na da mafi karancin GDP na kowane mutum duk da cewa ita ce kasar da ke kan gaba wajen samar da mai a Afirka, kuma mamba ce a kungiyar kasashe masu fitar da man Fetur (OPEC).

Agba ya ce, Nijeriya ita ce kasa mafi girma, kuma mafi yawan tattalin arziki a Afirka, tare da GDP na dala biliyan 446 da yawan jama’a kimanin miliyan 206 a shekarar 2020.

Haka zalika, Ministan ya ce, yawan kudin shigar da take samu na dala 2,156.51 a shekarar 2020, kaso 19 ne kawai na adadin duniya.

“Nijeriya, kamar sauran kasashe masu tasowa, tana fuskantar matsaloli masu daure kai wadanda za su hana ta cimma burinta na ci gaba,” in ji shi.

A cewarsa, MTNDP za ta kafa kakkarfan tushe don fadada tattalin arziki, ta hanyar bunkasar MSME da kuma yanayin kasuwancin da zai fi jurewa.

Ya ce, manyan tsare-tsaren tattalin arzikin mai na bayan Nijeriya sun hada da nazarin Ajandar 2063 na kungiyar tarayyar Afirka (AU), da kungiyar raya tattalin arzikin Yammacin Afirka (ECOWAS) ta 2050 da kuma cigaba (SDG) 2030.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Hukumar Kudade Ta Duniya Ta Saka Jarin Yuro Miliyan 20 A Nijeriya

Next Post

Nijeriya Za Ta Samar Da Abinci Mai Gina Jiki Don Rage Aibun Yunwa

RelatedPosts

Kudade

Akwai Isassun Kudade Ga Masu Kasuwanci, Cewar CBN

by Muhammad
3 weeks ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad, Babban bankin Nijeriya (CBN) ya kawar...

Gwamnatin Nijeriya Ta Samu Rancen Dala Biliyan 2.5 Don Aikin Jirgin Kasa Na Legas-Ibadan

Gwamnatin Nijeriya Ta Samu Rancen Dala Biliyan 2.5 Don Aikin Jirgin Kasa Na Legas-Ibadan

by Sulaiman Ibrahim
3 weeks ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad Ministan sufuri, Rotimi Amaechi, ya ce,...

Hukumar EFCC Ta Gargadi Masu Amfani Da Na’urar ‘POS’ Kan Gurbatacciyar Hada-hada

Hukumar EFCC Ta Gargadi Masu Amfani Da Na’urar ‘POS’ Kan Gurbatacciyar Hada-hada

by Sulaiman Ibrahim
3 weeks ago
0

Daga Mahdi M. Muhammad Hukumar nan da ke yaki da...

Next Post
Farashin

Nijeriya Za Ta Samar Da Abinci Mai Gina Jiki Don Rage Aibun Yunwa

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version