• Leadership Hausa
Monday, January 30, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai

Wa’adin Canjin Kudi: Buni Ya Nemi CBN Ya Ƙara Wa Jihar Yobe Lokaci

Ya Ce A Cikin Kananan Hukumomin Jihar 17, 4 Kacal Suke Da Banki

by Muhammad Maitela
1 week ago
in Labarai
0
Wa’adin Canjin Kudi: Buni Ya Nemi CBN Ya Ƙara Wa Jihar Yobe Lokaci

Gwamnan jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni, ya bukaci Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya kara wa al’ummar jihar Yobe wa’adi na daban, da zai bayar da damar canza tsoffin takardun kudadensu, sabanin 31 ga watan Janairun da ya saka da farko.

Gwamnan ya bayyana hakan a sanarwar manema labaru, ranar Lahadi, mai dauke da sa-hannun Daraka Janar kan hulda da yan jaridu da Kafafen yada labaru, Mamman Mohammed, inda ya ce Gwamna Buni ya bayyana cewa neman ƙarin wa’adin ya zama dole sakamakon yadda jihar ke fama da karancin bankuna.

Gwamna Buni ya kara da cewa, kananan hukumomi hudu ne kacal cikin 17, a fadin jihar suke da bankuna, al’amarin da ya ce zai yi wahala mutane su samu damar canja kudaden su a kwanaki 13 da suka rage a wa’adin da Babban Bankin Nijeriya ya gindaya.

“Sannan kuma wasu daga cikin bankunan da suke da rassa a wasu kananan hukumomin, dole ya sa sun rufe sakamakon rikicin Boko Haram da ya yi kamari, kuma har yanzu basu sake bude su ba a fadin jihar.”

“Saboda haka muna kyautata zaton CBN zai kula wajen bai wa irin wadannan wurare kulawa ta musamman sakamakon bukatu na musamman, domin kaucewa jawo asarar kudaden jama’a.”

Labarai Masu Nasaba

DSS Ta Kama Wasu Ma’aikatan Banki Masu Hada-hadar Sayar Da Sabbin Kudaden Naira

Tsohon Firaministan Kenya, Odinga, Ya Iso Nijeriya Don Halartar Taron LEADERSHIP Na 14

“Kuma muna kira ga CBN da sauran bankunan Kasuwanci su kalli wannan bukata ta jama’a cikin gaggawa wajen nemawa al’umma mafita tare da dakile halin fargaban da ake ciki.”

“A matsayinsa na mai sanya ido, yana da kyau Babban Bankin Nijeriya ya tabbatar cewa bankunan Kasuwanci sun bude rassan su a shalkwatar kananan hukumomin saboda a halin yanzu zaman lafiya ya samu a fadin jihar Yobe.” In ji Gwamna.

  • Naja’atu Ta Yi Murabus Daga Kwamitin Yakin Zaben Tinubu, Ta Fice Daga APC

 

Bugu da kari, Gwamna Buni ya kara da cewa, ci gaban da ake samu ta fannin tsaro a jihar Yobe da Arewa Maso Gabas baki daya, babu wata fargabar da za ta hana bankuna su sake bude rassan su a shalkwatar kananan hukumomin da manyan garuruwa.

Har ila yau, Gwamna Buni ya sake nanata cewa, akwai fargaba matikar ba a dauki matakin gaggawa ba, saboda ko shakka babu jama’a da dama za su fuskanci barazanar karayar tattalin arziki, da dalilin canjin kudin.

  • https://leadership.ng/cbn-warns-against-rejection-of-old-naira-notes/

 

“Sannan a matsayinmu na gwamnati, wajibi ne mu yi dogon nazari don kaucewa kalubalen da zai jawo, wanda lalle akwai bukatar CBN, Babban Bankin Nijeriya ya dubi lamarin nan tare da daukar matakan da suka dace wajen shawo kan matsalar.” In ji Gwamna Buni.

Previous Post

Atiku: ‘Yan Nijeriya, Tsakanin Mulkin PDP Da APC, Wanne Ya Fi Bala’i?

Next Post

An Yi Murnar Shiga Sabuwar Shekarar Zomo Ta Kasar Sin A Fadin Duniya

Related

DSS Ta Kama Wasu Ma’aikatan Banki Masu Hada-hadar Sayar Da Sabbin Kudaden Naira
Labarai

DSS Ta Kama Wasu Ma’aikatan Banki Masu Hada-hadar Sayar Da Sabbin Kudaden Naira

3 hours ago
Tsohon Firaministan Kenya, Odinga, Ya Iso Nijeriya Don Halartar Taron LEADERSHIP Na 14
Labarai

Tsohon Firaministan Kenya, Odinga, Ya Iso Nijeriya Don Halartar Taron LEADERSHIP Na 14

4 hours ago
Jirgin Kasan Kaduna-Abuja Ya Dawo Aikin Jigilar Fasinjojinsa Bayan Hatsarin Da Ya Yi
Labarai

Jirgin Kasan Kaduna-Abuja Ya Dawo Aikin Jigilar Fasinjojinsa Bayan Hatsarin Da Ya Yi

5 hours ago
2023: Laifin Me Na Yi Wa Mutanen Da Suke Cin Amana Ta —Tinubu
Labarai

2023: Laifin Me Na Yi Wa Mutanen Da Suke Cin Amana Ta —Tinubu

8 hours ago
Gwamnatin Kano Ta Shirya Tarbar Zuwan Buhari Kano Bayan Kara Wa’adin Daina Tsaffin Kudi
Labarai

Gwamnatin Kano Ta Shirya Tarbar Zuwan Buhari Kano Bayan Kara Wa’adin Daina Tsaffin Kudi

9 hours ago
Buhari Ya Nada Dogara A Matsayin Sabon Darakta Janar Na Hukumar NYSC
Labarai

Buhari Ya Nada Dogara A Matsayin Sabon Darakta Janar Na Hukumar NYSC

20 hours ago
Next Post
An Yi Murnar Shiga Sabuwar Shekarar Zomo Ta Kasar Sin A Fadin Duniya

An Yi Murnar Shiga Sabuwar Shekarar Zomo Ta Kasar Sin A Fadin Duniya

LABARAI MASU NASABA

Gogewar Kasar Sin A Fannonin Ilimi Da Binciken Kimiyya, Abun Karfafa Gwiwa Ne Ga Kasashen Larabawa 

Gogewar Kasar Sin A Fannonin Ilimi Da Binciken Kimiyya, Abun Karfafa Gwiwa Ne Ga Kasashen Larabawa 

January 30, 2023
Babban Kwamatin Ayyuka Na Jam’iyyar PDP Na kasa Ya Gana Da ‘Yan Takarar Gwamna Na Jam’iyyar

‘Yan Majalisar Tarayya 3 Na Jam’iyyar APC Sun Koma Jam’iyyar PDP A Jihar Katsina

January 30, 2023
Kasar Sin Ta Tsawaita Wasu Dabarunta Na Kudi

Kasar Sin Ta Tsawaita Wasu Dabarunta Na Kudi

January 30, 2023
DSS Ta Kama Wasu Ma’aikatan Banki Masu Hada-hadar Sayar Da Sabbin Kudaden Naira

DSS Ta Kama Wasu Ma’aikatan Banki Masu Hada-hadar Sayar Da Sabbin Kudaden Naira

January 30, 2023
Tsohon Firaministan Kenya, Odinga, Ya Iso Nijeriya Don Halartar Taron LEADERSHIP Na 14

Tsohon Firaministan Kenya, Odinga, Ya Iso Nijeriya Don Halartar Taron LEADERSHIP Na 14

January 30, 2023
Jirgin Kasan Kaduna-Abuja Ya Dawo Aikin Jigilar Fasinjojinsa Bayan Hatsarin Da Ya Yi

Jirgin Kasan Kaduna-Abuja Ya Dawo Aikin Jigilar Fasinjojinsa Bayan Hatsarin Da Ya Yi

January 30, 2023
Tinubu Ya Godewa Buhari Kan Amincewa Da Kara Wa’adin Kwanakin Daina Karbar Tsoffin Kudade

Tinubu Ya Godewa Buhari Kan Amincewa Da Kara Wa’adin Kwanakin Daina Karbar Tsoffin Kudade

January 30, 2023
2023: Laifin Me Na Yi Wa Mutanen Da Suke Cin Amana Ta —Tinubu

2023: Laifin Me Na Yi Wa Mutanen Da Suke Cin Amana Ta —Tinubu

January 30, 2023
Rundunar ‘Yansandan Jihar Kano Ta Cafke Jarumar TikTok Murja Ibrahim Kunya

Ina Addu’ar Allah Ya Saukar Min Da Cutar Da Za Ta Sa Na Shiryu – Murja Ibrahim Kunya

January 30, 2023
Gwamnatin Kano Ta Shirya Tarbar Zuwan Buhari Kano Bayan Kara Wa’adin Daina Tsaffin Kudi

Gwamnatin Kano Ta Shirya Tarbar Zuwan Buhari Kano Bayan Kara Wa’adin Daina Tsaffin Kudi

January 30, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.