Hussaini Yero">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Wadanda  Suka Yi Garkuwa Da ‘Ya’yan Shugaban Jam’iyyar APC A Zamfara Sun Nemi Naira Milyan 50

by Hussaini Yero
January 16, 2021
in RAHOTANNI
2 min read
Garkuwa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Wadanda su ka yi garkuwa da ‘ya’yan shugaban jam’iyyar APC na karamar hukumar Maru, ta jihar Zamfara, Alhaji Sani Gyare Kadauri, sun nemi a ba su kudin fansa Naira miliyan hamsin na yaran bakwai da suka sace a ranar Juma’a da ta gabata.

Wadanda suka sace sun hada da, Bashar da Abubakar da Haruna da Habibah da Sufyanu da Mubarak da Armayau da Masu garkuwa  sun sace su ne a ranar Juma’ar da ta gabata a kauyen Kadauri.

samndaads

Mahaifin yaran ya bayyana  wa manema Labarai ta waya cewa, Masu garkuwa sun kirashi sun gaya masa ya kawo kudin miliyan hamsin ko ya rasa ‘ya’yan nasa.

“Sun kira ni sun tambaye ni in biya niara miliyan N50m don sakin yarana su bakwai kuma sun yi gargadin cewa za su kashe su idan ba a biya kudin a kan lokaci ba,” in ji shi.

“Hatta Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Bala Bello Maru, wanda ya fito daga Karamar hukuma ta, bai zo gidana don tausaya min ba, kuma bai kira ni a waya ba.”

Ya kuma koka kan yadda Shugaban Karamar hukumar, Alhaji Salisu Dangulbi, shi ma bai tuntube shi kan lamarin ba.

“Ina jin damuwa sosai;  Ina jin kamar ni cikakken bako ne kuma ban san abin da zan yi a wannan lokacin ba, saboda ba zan iya biyan kudin da wadannan mutane marasa zuciya suke nema ba, “inji Gyare.

Ya lura cewa ba zai iya tara kudin da Masu garkuwa suke nema ba ko da kuwa ya sayar da duk kadarorinsa, yana mai cewa, “Na yi masu bayanin hakan ne a kan wayar amma kawai sai suka yi min dariya.”

Gyare ya nuna rashin jin dadinsa game da halin rashin yarda da halin da hukumomin da abin ya shafa ke nunawa na kare rayuka da dukiyoyin ‘yan Nijeriya.

Ya ce ‘yan ta’addan sun yi awon gaba da yaran nasa ba tare da turjiya daga jami’an tsaro ba, wadanda aka sanar da su abin da ke faruwa a kauyen.

A cewarsa, lokacin da Masu garkuwa suka shiga kauyen, an sanar da’ yan sanda amma ba su zo wurin ba sai bayan awa uku bayan sun gama aikinsu suka tafi.

‘Yan jaridu suka  tuntubi kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Mohammed Shehu, ya ce yana sane da yaran da aka sace, amma ba shi da masaniyar kudin fansa na miliyan  N50m da  Masu garkuwa suka nema.

SendShareTweetShare
Previous Post

‘Yan Mulkin Mallaka A Kasashen Afirka (1)

Next Post

Masana Sun Nuna Damuwa Kan Karbo Bashin Naira Tiriliyan 5.39 Domin Cike Gibin Kasafin Kudi

RelatedPosts

Neja

Tsaro; Sakataren Gwamnatin Neja Ya Nemi ‘Yan Bindiga Su Aje Makamai

by Hussaini Yero
4 days ago
0

Daga Muhammad Awwal Umar, Sakataren gwamnatin Neja, Ahmed Ibrahim Matane...

Tinubu

Sanata Tinubu Ya Bukaci A Kara Samar Da Zaman Lafiya Tsakanin Al’umma

by Hussaini Yero
4 days ago
0

Daga Idris Aliyu Daudawa, Jagoran jam'iyyar babbar jam’iyya mai mulkin...

Miyagun Kwayoyi

Shugaban NDLEA Ya Yi Alkawarin Fattatakar Dillalan Miyagun Kwaya A Nijeriya

by Hussaini Yero
4 days ago
0

Daga Bello Hamza, Shugaban hukumar NDLEA, Brig. Gen. Buba Marwa...

Next Post
Kisa A Arewa

Masana Sun Nuna Damuwa Kan Karbo Bashin Naira Tiriliyan 5.39 Domin Cike Gibin Kasafin Kudi

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version