Wadanne Damammaki Da Aka Samu Cikin Abubuwan Da Aka Nuna A Karon Farko A Duniya A CIIE?
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wadanne Damammaki Da Aka Samu Cikin Abubuwan Da Aka Nuna A Karon Farko A Duniya A CIIE?

byCGTN Hausa
2 years ago
CIIE

A yayin bikin baje kolin kasa da kasa na kayayyakin da ake shigo da su kasar Sin CIIE karo na shida da ake gudanarwa a birnin Shanghai, an baje sabbin kayayyaki masu dimbin yawa, kamar abin tsaftace kujerun zama a falo, da labulaye ba tare da cire su daga muhallin su ba, da na’urar zamani ta yin kwalliyar fuska, wadanda suke kunshe da manyan fasahohi kamar basirar dijital, da fasahohi marasa gurbata muhalli.

A yayin bikin CIIE na wannan karo, an kuma nuna sabbin kayayyaki, da fasahohi, da ma hidimomi har guda 442, wadanda aka fitar da su a karon farko. Kuma a bukukuwan CIIE da aka gudanar cikin shekaru 5 da suka wuce, an riga an fitar da sabbin kayayyaki, da fasahohi, da hidimomi har kusan 2000. To ko me ya sa aka fitar da sabbin kayayyaki a bikin na CIIE?

  • Manzon Musamman Na Sin Kan Batun Yankin Gabas Ta Tsakiya Zai Halarci Taron Tallafin Jin Kai A Gaza
  • Masu Kada Kuri’a: CIIE Na Kara Kuzari Kan Tattalin Arzikin Duniya

Amsar ita ce Sin tana da yawan al’umma fiye da biliyan 1.4, wadanda suka hada da masu samun matsakaitan kudin shiga fiye da miliyan 400, wanda hakan ya samar da wani babban wurin gwaji, da wurin fitar da sabbin fasahohi, da kayayyaki na kasa da kasa. Kayayyakin dake cike da basirar kirkire-kirkire, sun kyautata rayuwar al’umma, ta yadda suke cika bukatun masu saye-saye na Sin.

A sa’i daya kuma, yadda kasar Sin ta samu nasarar aiwatar da manyan tsare-tsaren raya kasa ta hanyar yin kirkire-kirkire, ya samar da damammaki ga ‘yan kasuwan waje wajen yin kirkire-kirkire. A watan Satumban bana, rahoton da kungiyar kiyaye ikon mallakar fasaha ta duniya ta bayar ya nuna cewa, Sin tana matsayi na 12 a duniya, kuma ita ce kasa daya tilo mai matsakaicin kudin shiga a cikin kasashe 30 na farko.

Har ila yau, ci gaban kasar Sin mai inganci yana ta jan hankalin duniya, Da yawa daga cikin masu halartar CIIE sun kafa cibiyoyin nazari a Sin.

Ana hasashen cewa, karin kamfanonin duniya za su zuba jari a Sin ta hanyar CIIE, inda ba oda, ko kasuwa, ko sabbin tunani kadai ba ne za su samu, har ma da damammakin da zamanintarwa irin na Sin ke kawowa. (Safiyah Ma)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa
Daga Birnin Sin

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Next Post
Gwamna yusuf

Gwamnatin Kano Za Ta Kashe Sama Da Naira Biliyan 40 Wajen Aiwatar Da Manyan Ayyukan Raya Jihar

LABARAI MASU NASABA

Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version