Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

byCGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
Kasa

A duk ranar 19 ga watan Agusta ne ake bikin ranar jin kai ta duniya, ranar da asali aka kirkire ta domin alhinin jami’an jin kai da aka kashe, ko aka jikkata yayin da suke bakin aiki, tare da jinjinawa daukacin ma’aikatan jin kai da na lafiya dake ci gaba da samar da hidimomin ceton rayukan jama’a, da kare mutanen dake cikin matsanancin yanayin bukatar agaji.

 

To sai dai kuma a bana, bikin ranar ya zo daidai gabar da yanayin da ake ciki, ke kara tunatar da duniya irin muggan laifukan da ake aikatawa ga bil’adama musamman a yankin gabas ta tsakiya.

  • Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025
  • Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Tashe-tashen hankula na ci gaba da bazuwa tun daga Gaza, zuwa Sudan, da Syria da Yemen, lamarin da ya haifar da mummunan bala’i da yanayin bukatar jin kai, wanda ke nuni da cewa duk da ci gaban da duniya ke samu ta fuskar ilimi, kimiyya da fasahohi, a hannu guda bil’adama na ci gaba da fuskantar manyan kalubalen rayuwa da suka hada da yunwa, da muzgunawa da rashin tsaron rayuka.

 

Alkaluman baya bayan nan na nuna cewa a Gaza, wurin da kusan mutane miliyan biyu ke matse a yankin da bai wuce sakwaya mita 45 ba, adadin mutane da yaki ya hallaka ya munana. Mahukuntan lafiya a wurin na cewa an hallaka sama da mutane 62,000, tun sake barkewar tashin hankali a zirin, ciki har da yara kanana kimanin 18,000. Baya ga karasa gurgunta tsarin kiwon lafiyar birnin, da yunwa da ta haifar da mace-macen jama’a.

 

Haka ma abun yake a Sudan, kasar da tashe-tashen hankula suka raba mutane kimanin miliyan 12 da muhallansu, adadin da ya kai kusan daya bisa hudu na daukacin jama’ar kasar. Wadannan misalai ne na irin matsanancin hali da al’ummun kasashen Yemen da na Syria ke fuskanta, karkashin ayyukan bil’adama ba wai bala’i daga indallahi ba!

 

Don haka, a wannan gaba da ake waiwaye-adon-tafiya, game da wadannan matsaloli na jin kai dake addabar wasu duniya, ya wajaba sassan kasa da kasa, su sauke nauyin dake wuyansu na raya ruhin jin kan bil’adama, ta hanyar shiga tsakani, da warware rigingimu, da gudanar da shawarwarin zaman lafiya, da tallafawa ma’aikatan jin kai, ta yadda za su gudanar da ayyukansu lami lafiya. A hannu guda kuma, a himmatu wajen magance tushen aukuwar tashin hankali a dukkanin sassan duniya, ta yadda za a gudu tare a tsira tare.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?
Daga Birnin Sin

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
Next Post
Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version