Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Wakilcin Nura Nakowa Alheri Ne Ga Al’ummar Rano – Idi Gwangwan

by
2 years ago
in RIGAR 'YANCI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

Shugaban jam’iyyar APC na karamar hukumar Rano, Alhaji Idi Gwangwan ya bayyana dan majalisarsu na jiha mai wakiltar yankin, Hon.Nura Alhasan Nakowa da cewa, wakili ne nagari dake sauke nauyin al’ummarsa.

Alhaji Idi Gwangwan ya ce, zaben da al’ummar Rano suka yi masa sunyi zabe na alheri kuma shine dan auta me karamin shekaru a majalisar jihar Kano. Amma yana da tunani da hangen nesa basu taba zaton zai zame musu mafi alkhairi a karamar hukumar ba. Domin bai wuce kwanaki 30 da zuwa majalisa ba yasa aka yi aikin ido na mutane 339 bayan ‘yan kwanaki da wannan ya raba Babura ya sake raba tallafin ya kira mata guda 283 kowacce ya bata turmin atamfa bayan aikace-aikace wadanda yake na Makarantu da Masallatai makarantun islamiyya irin abubuwa da ya yi ba abin da za su ce dashi sai dai Allah ya saka da alkhairi.
Ya ce, kamar yanda a baya suka zabi tsohon kakakin majalisar Kano. Right Hon Kabiru Alasan kwalliya ta biya sabulu yanzu ma ta biya suna godiya akai. Irin tarbiyya da dan majalisar Rano Hon. Nura Nakowa ya samu daga manyansa yana kula da shawarar manya saboda haka duk abinda ya yi ba mamaki suna godiya da fatan Allah ya saka masa da alkhairi.
Idi Gwangwan ya ce, su a Rano ko gobe aka ce a sake fitowa sunanan yanda suka zabi tsohon Kakakin majalisar Kano sau biyu shekara Takwas sannan ya tafi majalisar tarayya shima sunanan za su bashi goyon baya da yardar Allah.
Alhaji Idi Gwangwan ya ce, dan majalisar nasu ya gudanar da kudurce-kudurce a majalisa ba abinda yafi damun al’ummar Rano samar da ruwansha Hon. Nura Nakowa yakai kuduri Gwamna ya sawo manyan injuna guda uku sunanan an kaisu Tiga. Ya kuma sake kai yanda za’a ga an hada injunan sukai ruwa daga Tiga zuwa Rano har Kibiya.
Ya ce, bayan haka akwai kudurin masarauta da Allah ya tabbatar da da sauran kudure-kudure na samar da taki dan habaka noma da kuduri na fadada Asibiti na Rano ana ta aikace-aikace ansa gadaje sama da 400 a ciki.
Idi Gwamgwan ya gode wa al’ummar Rano da kuma kira a dada taya Gwamna da addu’a suna kuma fata wannan masarauta Allah ya daukaketa ya jikan Sarkin Rano da sauran sarakai ya kawo daukaka da cigaba al’ummar Rano da jihar Kano.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Boko Haram: Akwai Kananan Hukumomi Biyar Da Ba A Shiga A Borno

Next Post

Al’ummar Kabo Na Alhini Da Jimamin Rasuwar Abba Salisu

Labarai Masu Nasaba

Zamfara

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

by
1 year ago
0

...

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

by
1 year ago
0

...

APC

Sanata Al-Makura Ya Cancanci Rike Kujerar Shugabancin APC, Inji Gwamna Sule

by
1 year ago
0

...

Kebbi

Bagudu Ya Bukaci ’Yan Nijeriya Su Zama Masu Kishin Kasa A Shafukan Sada Zumunta

by
1 year ago
0

...

Next Post
Al’ummar Kabo Na Alhini Da Jimamin Rasuwar Abba Salisu

Al'ummar Kabo Na Alhini Da Jimamin Rasuwar Abba Salisu

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: