Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Walin Zazzau Suleja Ya Zama Sabon Shugaban Jami’ar Kimiyya Da Fasaha Ta Minna

by Tayo Adelaja
September 20, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Awwal Umar, Minna

Gwamnan Neja Ya jawo hankalin sabon Shugaban Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta gwamnatin tarayya, Farfesa Abdullahi Bala da ya zama mai jagoranta jami’ar akan gaskiya da amana a lokacin aiwatar da nauyin da aka dora masa

samndaads

Ya ce, wannan nauyin da aka dora mai ya biyo bayan jajircewarshi da kwazo akan aiki da ya nuna a baya.

Bayanin hakan na kumshe a wata takardar taya murna ga sabon shugaban jami’ar da Jami’in hulda da manema labarai na mai girma gwamnan Jihar Neja, ya aikewa manema labarai.

Ya ci gaba da cewa; “Za ka bada gudunmawa na lokacinka ga shugabancin wannan jami’ar, don dawo da martabar ilimi a kasa, ta yadda tsarin ilimi a Jami’ar FUT da ke minna zai samu tagomashi da bunkasa don samun daidaito da tsarin kasa da ma duniya baki daya.

“Hukumar gudanarwar jami’ar ta yi farin ciki da hada hannu da kai wajen samar da zaman lafiya a Jami’ar wanda zai janyo hankalin dalibai daga ko ina a cikin kasa don sha’awar shigowa don cigaba da neman ilimi.  Gwamnan ya cigaba da cewar ya kamata sabon shugaban jami’ar kasancewarsa cikakken dan jiha da ya tabbatar jihar ta cike gurabun da aka bar ma ta, tare da kirkiro gurabun ayyuka ga jama’ar jiha. Kasancewar ka dan kasa na gari, wanda ya kwatanta a ayyukansa na baya, lallai ka zama jakadar jiha ta yadda gwamnatin jiha za ta hada hannu da jami’ar don bunkasa tsarin ilimin jami’a.”In ji jami’in huldan

Farfesa Abdullahi Bala dai dan asalin jihar Neja ne daga karamar hukumar Suleja. Yayi mafi yawa na karantunsa a jami’ar Landan, kafin zuwansa kan wannan mukamin ma’aikaci ne a jami’ar ta Kimiyya da Fasaha (FUT) da ke Minna, ya taba rike mataimakin shugaban jami’ar kuma ya taba rike mataimakin shugaban jami’ar a bangaren gudanarwa, sannan memba a kwamitin gudanarwa na jami’ar. A na sa ran zai fara aiki 3 ga watan disamba na 2017, kuma shi ke rike da rawanin Walin Zazzau Suleja, yana da mata da yara.

SendShareTweetShare
Previous Post

Inuwar Matasa: Ko Matasa Na Iya Yin Takara?

Next Post

Buhari Ya Ce A Yi Sulhu Da Shugaban Koriya Ta Arewa

RelatedPosts

Buba Marwa Ya Zama Sabon Shugaban Hukumar NDLEA

Buba Marwa Ya Zama Sabon Shugaban Hukumar NDLEA

by Muhammad
12 hours ago
0

Daga Abba Ibrahim Gwale, Shugaban kasa Muhammad Buhari ya amince...

Kananan Hukumomin Jihar Kano

Yau Za A Yi Karon Batta A Zaben Kananan Hukumomin Jihar Kano

by Sulaiman Ibrahim
21 hours ago
0

 Jam’iyyu 11 ne za su fafata PDP Kwankwasiyya ta ce,...

Sojoji

Tsofaffin Sojoji Sun Nemi Karin Kudin Fansho

by Sulaiman Ibrahim
22 hours ago
0

Kungiyar tsofaffin sojoji ta kasa reshen jihar Anambra ta bukaci...

Next Post

Buhari Ya Ce A Yi Sulhu Da Shugaban Koriya Ta Arewa

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version