Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home DAGA BIRNIN SIN

Wang Yi: Taimakawa Kasashen Afirka Yaki Da COVID-19 Da Farfado Da Tattalin Arzikinsu Abu Ne Mafi Muhimmanci Ga Hadin-Gwiwar Sin Da Afirka

by Sulaiman Ibrahim
March 7, 2021
in DAGA BIRNIN SIN
2 min read
Wang Yi: Taimakawa Kasashen Afirka Yaki Da COVID-19 Da Farfado Da Tattalin Arzikinsu Abu Ne Mafi Muhimmanci Ga Hadin-Gwiwar Sin Da Afirka
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga CRI Hausa

Memban majalisar gudanarwar kasar Sin, kana ministan harkokin wajen kasar, Wang Yi ya bayyana cewa, a halin yanzu, taimakawa kasashen Afirka daban-daban wajen yaki da cutar COVID-19, gami da farfado da tattalin arzikinsu, abu ne mafi muhimmanci ga hadin-gwiwar Sin da Afirka.
A wajen taron manema labarai na zama na hudu na majalisar wakilan jama’ar kasar Sin karo na 13, Wang Yi ya nuna cewa, a bara, shugaba Xi Jinping ya jagoranci taron koli na musamman na hadin-gwiwar Sin da Afirka wajen dakile cutar COVID-19, inda ya sanar da wasu sabbin matakai na tallafawa Afirka. Kawo yanzu, kasar Sin ta turawa kasashen Afirka kayayyakin yaki da cutar cikin gaggawa har sau 120, gami da rukunonin kwararrun likitoci zuwa kasashe 15, tare kuma da samar da alluran riga-kafin cutar ga kasashen Afirka 35 da kungiyar tarayyar Afirka wato AU. Har wa yau, yanzu kasar Sin na samar da taimako wajen aikin gina babbar hedkwatar cibiyar dakile cututtuka masu yaduwa ta Afirka ko kuma Africa CDC a takaice, da gaggauta gudanar da hadin-gwiwa tsakanin wasu asibitocin Sin da Afirka 30.
Minista Wang ya kara da cewa, a bara ne aka cika shekaru 20 da kafuwar dandalin hadin-gwiwar Sin da Afirka wato FOCAC. Hadin-gwiwar Sin da Afirka ta zama abun koyi ga hadin-gwiwar da ake yi tsakanin kasashe masu tasowa. Kuma a shekarar da muke ciki, Sin da Afirka za su gudanar da sabon taron dandalin tattauna hadin-gwiwarsu a kasar Senegal, inda kasar Sin take sa ran amfani da wannan dama don marawa Afirka baya wajen ganin bayan cutar COVID-19, da gaggauta raya masana’antu, da kokarin dunkulewar nahiyar baki daya, da kuma taimaka mata wajen warware matsaloli bisa hanyar siyasa. Inganta hadin-gwiwar Sin da Afirka wajen raya shawarar “ziri daya da hanya daya”, da kara raya al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya tsakaninsu, zai samar da sabon kuzari ga ci gaban nahiyar Afirka mai dorewa. (Mai Fassara: Murtala Zhang)

SendShareTweetShare
Previous Post

Xi Ya Jaddada Muhimmancin Kiyaye Lafiyar Al’umma Da Gina Ingantaccen Tsarin Ilmi

Next Post

Karya Ba Za Ta Boye Nasarorin Da Aka Cimma Wajen Tabbatar Da Hakkin Dan Adam A Xinjiang Ba

RelatedPosts

Don Me Kasashen Duniya Suka Kara Maida Hankali Kan Dandalin Tattaunawa Na Kasashen Asiya A Bo’ao?

Don Me Kasashen Duniya Suka Kara Maida Hankali Kan Dandalin Tattaunawa Na Kasashen Asiya A Bo’ao?

by Sulaiman Ibrahim
10 hours ago
0

Daga CRI Hausa Bo’ao, wani karamin gari ne dake kudancin...

COVID-19: Annoba Ta Lamuke Amurkawa Sama Da Rabin Miliyan

COVID-19: Annoba Ta Lamuke Amurkawa Sama Da Rabin Miliyan

by Sulaiman Ibrahim
10 hours ago
0

Daga Ahmad Fagam Da alama dai har yanzu ba ta...

Ya Kamata Kasar Amurka Ta Koyi Fasahar Yin Takara Bisa Wani Nagartaccen Yanayi

Ya Kamata Kasar Amurka Ta Koyi Fasahar Yin Takara Bisa Wani Nagartaccen Yanayi

by Sulaiman Ibrahim
10 hours ago
0

Daga CRI Hausa Kwanakin nan, Le Yucheng, mataimakin ministan harkokin...

Next Post
Karya Ba Za Ta Boye Nasarorin Da Aka Cimma Wajen Tabbatar Da Hakkin Dan Adam A Xinjiang Ba

Karya Ba Za Ta Boye Nasarorin Da Aka Cimma Wajen Tabbatar Da Hakkin Dan Adam A Xinjiang Ba

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version