CRI Hausa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home DAGA BIRNIN SIN

Wani Masani A Afirka Ta Kudu Ya Godewa Kasar Sin Saboda Goyon-Bayanta Ga Afrika A Fannin Dakile Annobar COVID-19

by CRI Hausa
January 2, 2021
in DAGA BIRNIN SIN
1 min read
Wani Masani A Afirka Ta Kudu Ya Godewa Kasar Sin Saboda Goyon-Bayanta Ga Afrika A Fannin Dakile Annobar COVID-19
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Mista Emmanuel Matambo, masanin dangantakar Sin da Afirka, na jamiar KwaZulu-Natal ta Afirka ta Kudu, ya jinjinawa kasar Sin bisa dimbin nasarorin da ta samu a fannin kandagarkin annobar COVID-19 a shekara ta 2020, tare kuma da gode mata saboda cikakken goyon-bayan da take ba kasashen Afirka wajen inganta kwarewarsu a fannin yaki da annobar.

Emmanuel Matambo, ya bayyana haka ne yayin zantawarsa da babban rukunin gidan talabijin da rediyo na kasar Sin CMG.
Bazuwar annobar COVID-19 na babbar illa ga tattalin arzikin duniya, amma alkaluman kididdiga sun nuna cewa, tattalin arzikin kasar Sin ya samu ci gaba a cikin wasu manyan kasashe masu karfin tattalin arziki a duniya.
Dangane da haka, masanin ya yabawa kasar Sin saboda kirkire-kirkiren da take yi da kuma kuzarinta na raya tattalin arziki, inda ya bayyana Sin a matsayin abar koyi ga kasashen Afirka.
Ya kara da cewa, idan aka waiwayi abubuwan da suka wakana a shekara ta 2020, ana iya ganin cewa, kasar Sin da kasashen Afirka sun fadada hadin-gwiwa ta fuskar tattalin arziki, inda har suka rika goyon bayan juna da himmatuwa tare domin yaki da annobar COVID-19.
Ya ce, kasashen yammacin duniya sun saka siyasa a cikin batun annobar, da rura wutar rikicin kabilanci a cikin hadin-gwiwar Afirka da Sin. Amma kasar Sin tana marawa Afirka baya wajen ganin bayan annobar, da taimaka mata gina cibiyar dakile cututtuka masu yaduwa wato Africa CDC, alamarin da ya shaida irin zumunci mai karfi dake tsakaninsu. Mista Matambo ya kuma ce, akwai dadaddiyar alakar abota tsakanin Sin da Afirka, abun dake da muhimmancin gaske ga nahiyar Afirka. (Mai Fassara: Murtala Zhang)

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Shugaban CMG Ya Yi Kira Ga Kafafen Yada Labaran Yamma Su Gyara Kurakurensu Na Jirkita Gaskiyar Labaran Da Suka Shafi Kasasr Sin

Next Post

Dangantakar Sin Da Afrika Ta Kara Karfi Yayin Da Aka Fuskanci Kalubalen COVID-19

RelatedPosts

Matasan Sin Da Afrika Sun Tattauna Da Nufin Inganta Kare Halittu

Matasan Sin Da Afrika Sun Tattauna Da Nufin Inganta Kare Halittu

by CRI Hausa
8 hours ago
0

Matasan Sin da Afrika, sun gudanar da wani taro ta...

Alluran Rigakafin Kasar Sin Sun Sanya Kwarin Gwiwa Kan Yaki Da Annobar COVID-19 A Kasashe Da Yankuna Masu Yawa

Alluran Rigakafin Kasar Sin Sun Sanya Kwarin Gwiwa Kan Yaki Da Annobar COVID-19 A Kasashe Da Yankuna Masu Yawa

by CRI Hausa
8 hours ago
0

Annobar numfashi ta COVID-19 na ci gaba da yaduwa a...

Alluran Rigakafin Cutar COVID-19 Na Kasar Sin Na Taimakawa Kasashe Da Dama Yaki Da Cutar

Alluran Rigakafin Cutar COVID-19 Na Kasar Sin Na Taimakawa Kasashe Da Dama Yaki Da Cutar

by CRI Hausa
8 hours ago
0

A baya-bayan nan, wasu kasashe da yankuna sun amince da...

Next Post
Dangantakar Sin Da Afrika Ta Kara Karfi Yayin Da Aka Fuskanci Kalubalen COVID-19

Dangantakar Sin Da Afrika Ta Kara Karfi Yayin Da Aka Fuskanci Kalubalen COVID-19

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version