Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

‘Wasu Daga Cikin Sanatocin Da Suka Bar APC Na Shirin Dawowa’ Umar A Hunkuy

by
4 years ago
in LABARAI
2 min read
‘Wasu Daga Cikin Sanatocin Da Suka Bar APC Na Shirin Dawowa’ Umar A Hunkuy
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindigar Da Suka Sace Daliban Kwaleji 4 A Kaduna Sun Bukaci Kudin Fansa

Gwamnatin Ganduje Ta Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 A Kano

Shugaban masu rinjaye na Majalisar Dattijai, Ahmed Lawan, ya yi ikirari a ranar Laraba cewa, wasu daga cikin sanatocin da suka fice daga Jam’iyyar ta APC sun nuna aniyarsu ta sake dawowa cikin Jam’iyyar.
Lawan ya yi wannan ikirarin ne cikin wata tattaunawa da ya yi da manema labarai na fadar gwamnati jim kadan da ya jagoranci Sanatoci 43 na jam’iyyar ta APC wajen wani taron sirri tare da Shugaba Buhari, a fadar ta Shugaban Kasa.
Ya kuma yi zargin cewa, wasu ma Sanatocin Jam’iyyar PDP sun nu na aniyarsu ta shigowa cikin Jam’iyyar ta APC.
Ya ce, “Bari na gaya maku, ko a jiya awanni 24 da fadin sun canza shekan, mun tattauna da wasun su, sun kuma nu na aniyar su ta sake dawowa.
“Don haka muna yin duk abin da muke iyawa tare da shugabannin Jam’iyyarmu, domin ganin mun shawo kan ‘yan’uwan namu da suka fice su dawo a kwanan nan.
Lawan ya ce, abin da ya faru a zauren Majalisar, musamman ma Majalisar Dattawa, a ranar Talata, kamata ya yi ya zama wani sabani ne na iyalai, amma sai aka yi masa hukuncin da bai kamata ba.
“Amma yanzun duk mun yanke shawarar goyon bayan Shugaban kasarmu da kuma wannan gwamnatin domin mu cika dukkan alkawurran da muka dauka a lokacin yakin neman zabe.
Lawan ya ce, ‘yan Majalisar sun shaida wa Buhari hakikanin abin da ya faru a zauren majalisar, sun kuma tabbatar masa da har yanzun dai Jam’iyyar APC ne ke da rinjaye a cikin Majalisar, duk da ficewar da wasu suka yi.
Wani Sanata daga Jihar Kaduna, Shehu Sani, cewa ya yi, shi ba shi da sauran wani korafi, domin duk matsalar da yake da ita da Jam’iyyar an warware ta bakidayanta.
Ya ce, ai babu wata matsala a kan tayar da kayar baya, ya kara da cewa, ai ita kanta Jam’iyyar ta APC, alami ce ta tayar da kayar baya ai.
Shehu Sani, ya bayyana tabbacin da yake da shi na cewa, duk wasu rigingimun cikin jam’iyyar nan ba da jimawa ba za a warware su.
Ya ce, “Ina zaune ne a nan a matsayin dan Jam’iyyar APC a wannan majalisar ta Dattawa. Zaman da nake a nan ba yana nufin an gama warware matsalolin da nake fuskanta ne ba kacokam, amma dai ina da tabbacin a yanzun muna da shugaban da yake yin duk abin da yake iyawa na ganin ya warware dukkanin sabanin da har ya kai ga tayar da kayar bayan.
“Ina da tabbacin abin da muka tattauna a nan yana bayar da tabbaci ne na kwantar da duk wata kura da ta tashi, wacce har ta kai ga matsayin da muke cikinsa a yau din nan.
‘Ina da tabbacin Shugaban Jam’iyyarmu zai iya warware dukkanin matsalolin.”
Shugaban Jam’iyyar, Adams Oshiomhole, cewa ya yi, abin farin ciki ne da na ji daga bakin shugaban masu rinjaye cewa, har yanzun dai mune muke da rinjaye a cikin Majalisar.
Tsohon gwamnan na Jihar Edo, ya yi zargin cewa da yawa daga cikin wadanda suka bar Jam’iyyar duk an rude su ne.
Ya bayyana tabbacin da yake da shi na cewa, gaskiya za ta bayyana, ya kuma san duk za su dawo ne.
Ya ce, “Ai komai ya yi kyau. Muna da Sanatoci 53 daga cikin 107. A gaskiya hakan ya yi mana daidai. A nan da makwanni daya ko biyu, muna sa ran sake kama kujerun mu biyu na rashe-rashen da aka yi mana.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Kisan ‘Yansanda Ya Bazu Zuwa Jihar Ribas Umar A Hunkuyi

Next Post

Za Mu Karfafa Sadarwar Intanet Don Dacewa Da Fikirar ‘Yan Nijeriya –Osinbajo

Labarai Masu Nasaba

2023: Kwamishinonin Ganduje 7 Da Ya Amince Da Ajiye Aikinsu Da Ukun Da Ya Yi Watsi Da Su

‘Yan Bindigar Da Suka Sace Daliban Kwaleji 4 A Kaduna Sun Bukaci Kudin Fansa

by Abubakar Abba
15 mins ago
0

...

Gwamnatin Ganduje Ta Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 A Kano

Gwamnatin Ganduje Ta Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 A Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
56 mins ago
0

...

‘Yan Arewa Masu Kai Abinci Yankin Inyamurai Su Dakatar Saboda Kisa –Matasan Arewa A Kudu

‘Yan Arewa Masu Kai Abinci Yankin Inyamurai Su Dakatar Saboda Kisa –Matasan Arewa A Kudu

by
7 hours ago
0

...

EFCC Ta Bankado Gidaje 17 A Nijeriya Da Kasashen Waje Na Akanta Janar

EFCC Ta Bankado Gidaje 17 A Nijeriya Da Kasashen Waje Na Akanta Janar

by
19 hours ago
0

...

Next Post
Za Mu Karfafa Sadarwar Intanet Don Dacewa Da Fikirar ‘Yan Nijeriya –Osinbajo

Za Mu Karfafa Sadarwar Intanet Don Dacewa Da Fikirar ‘Yan Nijeriya –Osinbajo

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: