Wata Sabuwa: EFCC Ta Buɗe Littafin Kwankwaso
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wata Sabuwa: EFCC Ta Buɗe Littafin Kwankwaso

byAbubakar Sulaiman
1 year ago
EFCC

Hukumar yaƙi da masu yi wa tattalin arziƙin ƙasa zagon ƙasa (EFCC) ta fara bincike kan zargin karkatar da kuɗaɗen yaƙin neman zaɓe da jam’iyyar NNPP ta yi a zaben 2023. Binciken dai ya mayar da hankali ne kan zarge-zargen da ake yi wa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da tawagarsa, musamman gazawar kwamitin ayyuka na jam’iyyar a ƙarƙashin jagorancin Kwankwaso, wajen biyan wakilan jam’iyyar da suka yi aiki a lokacin zaɓen shugaban ƙasa da na gwamna.

EFCC na bin diddigin ikirarin da Kwankwaso da sakatariyarsa, Misis Folashade Aliu, suka yi na karkatar da kuɗaɗen ta hanyar wani asusun kamfen na sirri da kuma bayar da tallafi.

  • Sojojin Nijeriya Na Da Kwarewar Da Za Su Kawo Karshen Matsalar Tsaro –  Kwankwaso
  • APC Ta Zargi Kwankwaso Da Shirya Wa Ganduje Maƙarƙashiya Kafin Zaben 2027

Hukumar EFCC ta gayyaci Comrade Oginni Olaposi Sunday, sakataren jam’iyyar NNPP domin ya tabbatar da waɗannan zarge-zarge. A cewar wasu majiyoyi, koken Oginni ya shafi manyan masu sa hannun a asusun bankin NNPP da suka haɗa da Farfesa Rufa’i Alkali, Abba Kawu, da Dipo Olayokun.

EFCC na iya tsawaita bincikenta don bincikar Olayokun yadda ya tara dukiya da a Abuja cikin kankanin lokaci, wanda hakan ke nuni da cewa za a iya tafka maguɗi a harkar kuɗi da ke da nasaba da rawar da ya taka a matsayinsa na sa mai sa hannu.

Da yake tabbatar da ziyarar da ya kai shelƙwatar EFCC a kwanakin baya, Oginni ya bayyana cewa ya bayar da bayanan da suka dace da kuma ƙarin haske dangane da ƙarar.

Ya yabawa jami’an na EFCC bisa kwarewarsu tare da jaddada ƙudirin hukumar na yaki da cin hanci da rashawa. Yayin da Oginni ya tabbatar da binciken hukumar EFCC, ana sa ran nan ba da daɗewa ba za a gurfanar da Sanata Kwankwaso da sauran masu ruwa da tsaki kan zargin almundahanar Naira biliyan 2.5.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Rundunar PLA Za Ta Shiga Atisayen Hadin Gwiwa A Najeriya

Rundunar PLA Za Ta Shiga Atisayen Hadin Gwiwa A Najeriya

LABARAI MASU NASABA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version