Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home TATTALIN ARZIKI

Watakila Majalisa Ta Amince Da Kasafin 2021 Ranar 10 Ga Disamba

by Muhammad
December 2, 2020
in TATTALIN ARZIKI
2 min read
Disamba
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Ana tsammanin hadakar kwamitin majalisar dattijai da na majalisar wakilai za su amince da kasafin kudin shekarar 2021 a ranar 10 ga watan Disambar shekarar 2020. An bayar da rahoto cewa, har yanzu kwamitotin ba su mika rahoton ma’aikatu da rassa da cibiyoyin gwamnati ba. Sannan kuma majalisa ba za ta gudanar da sauraron jin ra’ayin mutane a kan kudaden sakamakon cutar Korona.

A ranar 20 ga watan Oktoba ce, kakakin majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila ya bayyana cewa, za a samu kammala komai kafin nan da zuwa ranar 3 ga watan Disamba. Amma a ranar 24 ga watan Nuwamba, Gbajabiamila ya koka ga yadda kashi 40 na kwamitocin ba su mika rahoto bag a majalisa.

samndaads

A ranar 22 ga watan Oktoba, majalisa ta dage zamanta domin a samu damar gudanar da daftarin kasafin kudin shekara 2021 na ma’aikatu da rassa da cibiyoyi. An dai fara mika rahoton ne tun a ranar 18 ga watan Nuwamba.

Da ya ke zantawa ga manema labarai a ranar Litinin, mataimakin shugaban kwamitin majalisa mika rahoton, Iduma Igariwey ya ce, “an dai takatar da sauraron jin ra’ayin mutane ne sakamakon cutaar Korona, wannan shi ne babban dalili. Ba mu da isasshen waje da zai dauki mutanen da muka saba gayyata.

“Mun yi tsammanin za mu yi amfani da zauran majalisa, amma sai muka ga hakan ba abu ba ne mai yuwuwa a gudanar da sauraron jin ra’ayin mutane a wurin. Wannan shi ne babban dalilin da muka dakatar da sauraron jin ra’ayin mutane wannan shekarar.”

Da yake gudanar da jawabi a kan rahoton kasafin kudin, Igriwey ya bayayyana cewa, “ana bayyana cewa, kwamitoci da dama sun mika rahoton kasafin kudinsu ga kwamitin amsar rahoton kasafin kudin.

“Ina tunanin abin da ya fi dacewa shi ne, majalisa ta kammala dukkan ayyukan kasafin kudin da shugaban kasa ta aike mata kafin karshen wannan shekara kamar yadda kundin tsarin mulki ta tanada.

“Kwamitocin  hadaka na majalisar dattijai da na wakilai na amsar rahoton za su kammala amsar dukkan wani rahoto a ranar 3 ga watan Disamba, yayin da majalisa za ta amince da kaafin kudin a ranar 10 ga watan Disamba,” in ji Igariwey.

SendShareTweetShare
Previous Post

Kiyaye Zaman Lafiyar Duniya Shine Burin Bai Daya Na Dukkan Bil’Adam -China

Next Post

Hawan Jini Lokacin Juna Biyu Da Abubuwan Da Suka Dace A Sani

RelatedPosts

Bangaren Gas A Nijeriya Na Cigaba Da Bunkasa – Mele Kyari

Bangaren Gas A Nijeriya Na Cigaba Da Bunkasa – Mele Kyari

by Sulaiman Ibrahim
8 hours ago
0

A kokarin da gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari ta mayar...

Katin Zama Dan Kasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Biya Ma’aikatan NIMC Albashi Na Musamman – Pantami

by Sulaiman Ibrahim
8 hours ago
0

Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani, Dakta Isa Ali Pantami,...

Ragin Harajin Shigo Da Motoci Zai Fara Aiki Daga Mako Mai Zuwa

Ragin Harajin Shigo Da Motoci Zai Fara Aiki Daga Mako Mai Zuwa

by Sulaiman Ibrahim
9 hours ago
0

A ranar Talata ce, hukumar Kwastom ta Nijeriya ta bayyana...

Next Post
Hawan Jini

Hawan Jini Lokacin Juna Biyu Da Abubuwan Da Suka Dace A Sani

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version