Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home KASASHEN WAJE

WHO Ta Kira Taron Gaggawa Kan Sabbin Nau’ikan Korona

by Sulaiman Ibrahim
January 16, 2021
in KASASHEN WAJE
1 min read
WHO
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Kwamitin kar ta kwana na hukumar lafiya ta duniya (WHO), ya kira wani taron gaggawa da ya tattauna matakan dakile barazanar da duniya ke fuskanta na sabbin nau’ikan cutar Korona da a yanzu ke yaduwa cikin gaggawa.

Yaduwar sabbin nau’ikan cutar ta Korona na cigaba da yin karfi a tsakanin kasashe a daidai lokacin da hukumomi suka sake kakaba dokokin takaita walwala ciki har da kulle yankuna da dama, sakamakon sake barkewar da annobar ta yi a zango na biyu.

samndaads

Batutuwa masu alaka da yaduwar sabbin nau’ikan cutar, aiwatar da shirin yiwa jama’a alluran rigakafi da kuma tsaurara yiwa matafiya gwajin cutar ne suka mamaye taron na WHO da ya gudana shekaran jiya Alhamis a Geneba.

WHO ta bayyana fargaba kan halin da Duniya ta tsinci kanta duk da matakin ci gaba da yiwa jama’a alluran rigakafin cutar ta Korona cutar da zuwa yanzu ta hallaka mutane miliyan 1 da dubu 954 da 336 tun bayan barkewarta cikin watan Disamban 2019 a yankin Wuhan na tsakiyar China.

Cikin rahotonta na mako mako, WHO ta ce sabuwar nau’in cutar da ta fara bulla a Birtaniya ta yadu zuwa kasashe 50, yayinda nau’in wadda aka gano a Afrika ta kudu kuma ta yadu a kasashe 20.

SendShareTweetShare
Previous Post

Babban Sabani A Tsakanin Jam’iyyun Amurka Zai Lalata Harkokin Kasa

Next Post

Biden Ya Kaddamar Da Shirin Tallafin Tattalin Arzikin Amurka Na $1.9tn

RelatedPosts

Ebola

WHO Ta Aike Da Tawaga Ta Musamman Guinea Da Kwango Don Yaki Da Ebola

by Muhammad
6 days ago
0

Hukumar lafiya ta Duniya WHO ta sanar da daukar tsauraran...

Somaliya

Majalisar Dinkin Duniya Ta Bukaci A Gaggauta Gudanar Da Zabe A Somaliya

by Muhammad
6 days ago
0

Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci bangarorin siyasar kasar Somalia da...

Alkalai

Alkalai Nijer Sun Gargadi ‘Yan Siyasa Su Daina Anfani Da Kalaman Kabilanci

by Muhammad
1 week ago
0

Alkali mai kare muradun hukuma (Procureur de la Republikue) ya...

Next Post
Tattalin Arzikin Amurka

Biden Ya Kaddamar Da Shirin Tallafin Tattalin Arzikin Amurka Na $1.9tn

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version