Wuraren Tarihi Da Suka Kamata Alhazai Su Ziyarta A Makkah Da Madinah
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wuraren Tarihi Da Suka Kamata Alhazai Su Ziyarta A Makkah Da Madinah

byBello Hamza
1 year ago
Tarihi

Akwai wuraren ajiye kayan tarihi masu dama da miliyoyin musulmi ke turuwar zuwa domin ilimantar da kasu a garin Al-Makkatu Mukarramah da Madinah Al-Munawara a duk shekara.

Bayan kammala ayyukan ibada na Umara ko Hajji tare da gudanar da dawafi da sa’ayi, alhazai kan kuma kosa su ziyarci wasu wurare masu muhimmanci a tarihin addinin musulunci.

  • Kamfanin Kera Motoci Masu Amfani Da Lantarki Na Sin Ya Shiga Kasuwar Kenya
  • Summer Davos: An Tattauna “Sababbin Damammaki A Kasar Sin”

Garuruwan biyu nada tarihin da ya wuce dubban shekaru, sun kuma danfaru da tarihin addnin musuluncin ne gaba daya, za kuma su ga yadda wasu al’adu da gine-ginen garuruwan suka canza a tsawon shekarun da suka wuce.

Wuri na farko da ya kamata Alhaji ya ziyarta shi ne unguwar da ake kira da ‘Unguwar Al’adu ta Hira’.

Domin fahimtar tarihi da muhimmancin wadannan garuruwan, dole mai ziyara ya yi nazarin muhimmancin su ga addinin musulunci, ana shawartar Alhazai su samu ziyartar wurare kamar Jannat Ul Mua’lla, Kogon Hira a kan dutsen ‘Jabal Al-Nour’, Dutsen Arafat da masallacin Ayesha.

Haka kuma a kusa da masallacin Haram akwai wuri mai muhimmanci da aka fi sani da Hudaibiyah, wurin da Manzo (SAW) ya sanya hannu a yarjejeniyar Hudaibiyah. Domin taskace tarihi da muhimmancin wurin a yanzu an gina masallaci a daidai wurin.

A shekarar 809, lokacin da aka fuskanci tsananin rashin ruwa a garin Makkah, Sarauniya Zubaida, matar Kalipha Harun Rashid, ta tafi aikin hajji, inda ta lura da wahalar da al’umma ke fama na rashin ruwa, a kan haka ta bayar da umarnin gina tafkin da aka fi sani da ‘Zubaida Canal’.

Yanzu shekaru dubbai ke nan alhazai na ci gaba da amfana da ruwan da ke fitowa daga tafkin.

Sai kuma dutsen Abu Kubais, inda mu’ujizar nan na wata ya faru, zai kuma ci gaba da kasancewa wani abin tunatarwa game da mu’ijizozin addinin musulunci.

Wani wurin da ya kamata alhaji ya ziyarta shi ne gidan tarihi na “Assalaamu Aleyka Ayyuhan Nabiyyu” a nan masu ziyara za su gani a bayyane tarihin rayuwar Annabi Muhammadu (SAW), ta hanyar kayayyakin da ya yi amfani da su a lokacin yana raye za su samu damar fahimmatar rayuwarsa da na kakanninsa, matansa, yaransa da sauran abubuwan da suka shafi gwagwarmayarsa ta tabbatar da addini. An kafa wannan gidan tarihi ne da hadin gwiwar malamai da masana fiye da 150 domin tabbatar da inganci da sahihancin abubuwan da aka samar a gidan.

Wani mai suna Ahmed Khanya ya bayyana cewa, shekararsa 15 yana aikin zagayawa da Alhazai wurare masu tsarki a garuwar Makkah da Madina.

“A kodayaushe Alhazai na jin dadin ziyartar wuraren da ke tattare da tarihin Manzon Tsira Muhammad Dan Abdullahi wanda hakan ke taimaka musu samun cikakkiyar fahimtar tarin addinin musulunci.”

Wasu wuraren sun kuma hada da kogon Hira a nan ne Manzon Allah (SAW) da Sahabinsa Abubakar suka boye a lokacin da Kuraishawa suka kai musu hari a yayin da suke hijira zuwa Madinah.

A garin Madinah, wanda ita ce ta biyu a daraja, musulmi shaukin ziyartar wuraren tarihi a garin da suka hada da, Masjid Al-Kiblatain, Masjid Abu Bakr, Masjid Al-Ahzab haka kuma akwai Masjid Al-Ghamamah duk da kankancinsa yana da muhimmanci don neman albarka a garin Madinah. Akwai kuma makabartar Baki’a da filin da aka tafka yakin Uhud.

Haka kuma akwai wuraren da aka yi wasu yake-yake masu matukar tarihi a addnini musulunci kamar yakin Khandak da aka yi a shekara ta 624 bayan hijira, a halin yanzu an gina babban masallaci a daidai wurin da aka yi yakin a tsakanin Musulman Madinah da Mushirikan Makkah.

Akwai kuma gonar Sayiddina Salman Farsi a Madinah inda tarihi ya nuna cewa, Manzon Allah (SAW) ya shuka dabino fiye da 300 domin ya ‘yantar da Salman Farsi daga bauta, daga nan kuma sai masallacin Kuba.

Ga wanda ya samu ikon zuwa kasa mai tsarki domin gudanar da ibadar Umara ko aikin Hajji ya kamata ya nemi a kai shi ziyara wadanna wuraren domin suna kara wa mutum Imani da fahimtar addninin musulunci, zai kuma fahimci irin canje-canje da aka samu a tsawon shekarun da suka wuce.

 

Yadda Aka Yi Dawafi Da Kananan Motoci A Hajjin Bana

Hukumar kula da harkokin masallaci mai alfarma da masallacin Manzo (SAW) ta kaddamar da yin dawafi ta hanyar amfani da wasu kananann motoci domin amfani da Alhazawa masi bukata ta musamman da kuma attajirai.

An jibge motocin ne a kofar shiga ta ‘Ajyad Escalators’ da ‘King Abdulaziz Gate Elebators’ da kuma ‘Umrah Gate Elebators’ ta yadda masu bukata za su gan su ba tare da wani wahala ba.

Motocin suna aiki a kullum na tsawon awa 12, daga karfe 4 na yamma zuwa karfe 4 na asuba ga duk wanda yake bukata.

Farashin hawa motar ya fara ne daga Riyal 25, ga duk mai bukatar yin dawafi ba tare da fuskantar cunkoso ba, kuma a cikin dan kankanin lokaci. Ana iya samun tikitin hawa motar a harabar Masallacin.

A wannan shekarar an yi amfani ne da kananan motoci 50 inda kowanne ke daukar mutum goma.

Saboda yawan al’umma da kuma irin cunkoson da ake fuskanta yayin gudanar da ibada, hukumomin kasar Saudiya na ci gaba da kirkiro da hanyoyin saukaka yadda ake gudanar da wasu ayyukan ibada yayin aikin hajji.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Mutane 2 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Su Da Hannu A Sace Mahaifiyar Rarara

Mutane 2 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Su Da Hannu A Sace Mahaifiyar Rarara

LABARAI MASU NASABA

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version