Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Rasha Ta Kafar Bidiyo
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Rasha Ta Kafar Bidiyo

byCGTN Hausa and Sulaiman
9 months ago
Xi

Shugaban kasar Sin, Xi Jinping, ya gana da takwaransa na kasar Rasha Vladimir Putin, ta kafar bidiyo da maraicen yau Talata 21 ga wata, a babban dakin taron alumma dake Beijing.

Shugaba Xi ya ce, a shekara ta 2024, kasashe Sin da Rasha sun zurfafa hadin-gwiwa da muamala a karkashin tsarin Majalisar Dinkin Duniya, da kungiyar hadin-gwiwa ta Shanghai wato SCO, da kuma kungiyar kasashen BRICS, inda suka bayar da gudummawa ga yin gyare-gyare gami da raya tsarin daidaita harkokin duniya.

  • Tsakanin Nijeriya Da BRICS+: Idan Zamani Ya Dinka Riga…
  • Samar Wa Nijeriya Sabon Kundin Tsarin Mulki Zai Magance Matsaloli – Moghalu

Shugaba Xi ya kuma jaddada cewa, bana ake cika shekaru 80, da jamaar kasar Sin suka samu galaba kan yakin kin maharan Japan, kana tsohuwar tarayyar Soviet ta samu nasara kan yakin kare kasa, kuma aka samu nasara kan yakin kin fascism a duk duniya. Kaza lika, lokaci ne na cika shekaru 80 da kafa Majalisar Dinkin Duniya. Ya ce ya dace kasashen Sin da Rasha su yi amfani da wannan dama, don kiyaye tsarin sassan kasa da kasa mai jigon MDD, da nasarorin da aka cimma daga yakin duniya na biyu, da taimakawa kasa da kasa su mutunta kaidoji da manufofin kundin tsarin mulkin MDD, da tsayawa ga muhimman kaidojin dangantakar kasa da kasa, da aiwatar da raayin cudanyar bangarori daban-daban a zahiri.

Shi kuwa shugaba Putin cewa yayi, yana farin cikin ganin ci gaban hadin-gwiwar kasashen biyu a fannonin tattalin arziki da kasuwanci da makamashi. Kasar Rasha na goyon-bayan cewa, Taiwan, yanki ne da ba zaa iya balle shi daga kasar Sin ba, kuma tana adawa da duk wani yunkuri na ware Taiwan daga kasar Sin. Ya ce Rasha na fatan karfafa hadin-gwiwa tare da kasar Sin a harkokin kasa da kasa, don haifar da da-mai-ido ga shimfida zaman lafiya da samar da ci gaba a duniya. (Murtala Zhang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?
Daga Birnin Sin

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
Next Post
Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Halarci Bikin Rantsar Da Trump

Mataimakin Shugaban Kasar Sin Ya Halarci Bikin Rantsar Da Trump

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version