CRI Hausa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home DAGA BIRNIN SIN

Xi Jinping Ya Shugabanci Taron Koli Na Kasar Sin Da Kasashen Tsakiya Da Gabashin Turai

by CRI Hausa
February 9, 2021
in DAGA BIRNIN SIN
2 min read
Xi Jinping Ya Shugabanci Taron Koli Na Kasar Sin Da Kasashen Tsakiya Da Gabashin Turai
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Yau Talata, aka gudanar da taron koli a tsakanin kasar Sin da kasashen tsakiya da na gabashin Turai ta kafar bidiyo, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya shugabanci taron tare da gabatar da muhimmin jawabi.


A yayin jawabinsa, Xi Jinping ya jaddada cewa, Sin da kasashen tsakiya da gabashin Turai suna nacewa ga mutunta juna, kuma suna hada kai ba tare da gindaya sharudda a fannin siyasa ba, kana Sin tana zaman daidai wa daida a tsakaninta da manya da kananan kasashe, da kuma tattaunawa tare kan manyan manufofin hadin kai, kafa dandalin hadin kai tare da kuma more nasarorin da aka cimma kan hadin kai.
Kasar Sin da kasashen tsakiya da na gabashin Turai suna cike da imanin cewa, yadda suke bude kofa ga juna, zai samar da damammaki kuma yadda suke hakuri da juna, zai taimaka wajen kara cudanya a tsakanin sassa daban daban, kuma wannan shi ne babban tushen kiyaye hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen dake tsakiya da gabashin Turai.
Baya ga haka, Xi Jinping ya nuna cewa, kasar Sin na shirin shigowa da kayayyaki da darajarsu ta zarce dala biliyan 170 daga kasashen na tsakiya da gabashin Turai a cikin shekaru biyar masu zuwa, da nufin habaka shigowa da kayayyaki daga kasashen.


Kana kuma Xi Jinping ya jaddada cewa, kasarsa za ta gaggauta kafa sabon tsarin ci gaba wanda zai mayar da hankali kan raya tattalin ariki a cikin gida don hade kasuwar cikin gida da ta ketare, domin samun ci gaba mai dorewa. Yadda kasar Sin ke samun dauwamammen ci gaba da yadda take bude kofa ga ketare, zai kara karfin farfadowa da kuma ci gaban tattalin arzikin duniya, kana zai habaka hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu.
Har illa yau, Xi Jinping ya bayyana cewa, kasar Serbia ta riga ta samu alluran rigakafin COVID-19 miliyan 1 daga kamfanonin kasar Sin, yanzu kuma kasar Hungary tana hadin gwiwa da kamfanonin rigakafin na kasar ta Sin. Dukkan kasashen dake tsakiya da gabashin Turai da suke bukatar hadin gwiwa a fannin allurar rigakafi, a shirye kasar Sin take ta himmatu wajen yin la’akari da haka.
A watan Afrilu na shekarar 2012, aka fara shirya tattaunawa a tsakanin shugabannin kasar Sin da kasashen tsakiya da gabashin Turai a Poland, kuma tun daga wannan lokacin, aka bullo da tsarin hadin gwiwa tsakanin bangarorin biyu a hukumance. Haka kuma tun bayan da aka kafa wannan tsari, cinikayya a tsakanin bangarorin biyu ya karu zuwa kashi 8 cikin 100, adadin da ya ninka sau 3 da wani abu, ya zuwa shekarar 2020 inda darajarsa ta zarce dala biliyan 100. (Mai fassara: Bilkisu)

SendShareTweetShare
Previous Post

Yerima Ya Zama Sabon Kakakin Rundunar Sojin Kasa Ta Nijeriya

Next Post

Ciki Da Gaskiya Wuka Ba Ta Huda Shi

RelatedPosts

Sin Ba Ta Son Yin Babakere, Mutunta Juna Da Hadin Kai Sune Ginshikan Makomar Huldar Sin Da Amurka

Sin Ba Ta Son Yin Babakere, Mutunta Juna Da Hadin Kai Sune Ginshikan Makomar Huldar Sin Da Amurka

by CRI Hausa
9 hours ago
0

Daga Amina Xu Kwanan baya, farfesa jami’ar Harvard Joseph S....

Karya Ba Za Ta Boye Nasarorin Da Aka Cimma Wajen Tabbatar Da Hakkin Dan Adam A Xinjiang Ba

Karya Ba Za Ta Boye Nasarorin Da Aka Cimma Wajen Tabbatar Da Hakkin Dan Adam A Xinjiang Ba

by CRI Hausa
9 hours ago
0

Daga CRI Hausa Kwanan nan ne kasar Amurka da sauran...

Wang Yi: Taimakawa Kasashen Afirka Yaki Da COVID-19 Da Farfado Da Tattalin Arzikinsu Abu Ne Mafi Muhimmanci Ga Hadin-Gwiwar Sin Da Afirka

Wang Yi: Taimakawa Kasashen Afirka Yaki Da COVID-19 Da Farfado Da Tattalin Arzikinsu Abu Ne Mafi Muhimmanci Ga Hadin-Gwiwar Sin Da Afirka

by CRI Hausa
9 hours ago
0

Daga CRI Hausa Memban majalisar gudanarwar kasar Sin, kana ministan...

Next Post
Ciki Da Gaskiya Wuka Ba Ta Huda Shi

Ciki Da Gaskiya Wuka Ba Ta Huda Shi

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version