Xi Jinping Ya Yi Jawabi Ta Kafar Bidiyo Ga Liyafar Murnar Cika Shekaru 60 Da Kulla Huldar Diplomasiyya A Tsakanin Sin Da Faransa
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Xi Jinping Ya Yi Jawabi Ta Kafar Bidiyo Ga Liyafar Murnar Cika Shekaru 60 Da Kulla Huldar Diplomasiyya A Tsakanin Sin Da Faransa

byCGTN Hausa
2 years ago
Xi

An gudanar da liyafar murnar cika shekaru 60 da kulla dangantakar diplomasiyya a tsakanin kasashen Sin da Faransa a babban dakin wasan kwaikwayo na kasar Sin yau Alhamis, inda shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da jawabi ta kafar bidiyo.

Xi Jinping ya yi nuni da cewa, a cikin shekaru 60 da suka gabata, dangantakar dake tsakanin Sin da Faransa, ta samar da moriya ga al’ummomin kasashen biyu, tare da ba da gudummawa wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da ci gaban duniya.
Xi ya jaddada cewa, ya kamata bangarorin biyu su ci gaba da raya dangantakar dake tsakaninsu don tinkarar rashin tabbas da duniya ke fama da shi, tare da daidaita dangantakar dake tsakanin Sin da Faransa. Ya kamata a yi amfani da damar shekarar raya al’adu da yawon shakatawa a tsakanin kasashen biyu da gasar wasannin Olympics ta birnin Paris, a matsayin damammaki na kara yin mu’amala da sada zumunta da juna. Kana ya kamata bangarorin biyu su yi kira ga martaba ra’ayin raya bangarori da dama na duniya da raya tattalin arzikin duniya cikin adalci, da ci gaba da samar da gudummawar Sin da Faransa wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da tinkarar kalubalen duniya, da kara yin hadin gwiwa da more damar samun ci gaba tare.

A nasa bangare, shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron shi ma ya yi jawabi ta kafar bidiyo, inda ya bayyana cewa, Faransa tana son yin aiki tare da kasar Sin wajen tinkarar kalubalen duniya da daidaita rikice-rikicen kasa da kasa tare. Shekarar 2024, shekara ce ta raya al’adu da yawon shakatawa a tsakanin Faransa da Sin, ya kamat a yi amfani da wannan dama wajen kara yin mu’amala a tsakanin jama’ar kasashen biyu musamman matasa don aza tubalin samun kyakkyawar makomar dangantakar dake tsakanin kasashen biyu. (Zainab Zhang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7
Daga Birnin Sin

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa
Daga Birnin Sin

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
Next Post
Tinubu Zai Kori Ministocin Da Ba Su Da Kwazon Aiki – Hadiza Bala Usman

Tinubu Zai Kori Ministocin Da Ba Su Da Kwazon Aiki – Hadiza Bala Usman

LABARAI MASU NASABA

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version