Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home DAGA BIRNIN SIN

Xi: Lafiya Ita Ce Alamar Farko Ta Jin Dadin Rayuwar Al’umma

by Sulaiman Ibrahim
March 24, 2021
in DAGA BIRNIN SIN
1 min read
Xi: Lafiya Ita Ce Alamar Farko Ta Jin Dadin Rayuwar Al’umma
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga CRI Hausa

Shugaban kasar Sin, kuma babban sakataren kolin JKS Xi Jinping, ya bayyana a jiya Talata cewa, lafiyar al’umma muhimmiyar alama ce ta yanayin jin dadin rayuwar su.
Xi wanda ya bayyana hakan yayin da ya ziyarci wani asibiti da ke birnin Sanming, dake lardin Fujian na gabashin kasar Sin, ya ce kasar sa ta ci gaba da samun bunkasuwar fannin kiwon lafiya, tun daga shekarar 1949, lokacin kafuwar jamhuriyar kasar Sin, kuma nasarar da kasar ta cimma a wannan fanni ta dara ta wasu daga kasashe masu ci gaba, musamman a fannin karuwar matsakaicin tsawon rayuwar al’umma. Ko da yake ya yi nuni da cewa, kawo yanzu, ba a kai ga cimma daidaito a ci gaban fannin ba da hidimar kiwon lafiya tsakanin sassa daban daban na kasar ba.
Shugaban na Sin ya kara da cewa, yayin aiwatar da shirin shekaru biyar biyar na tsarin samar da ci gaban kasar na 14, wato tsakanin shekarar 2021 zuwa 2025, Sin za ta kara azama wajen mayar da jama’a da lafiyarsu gaban komai, za kuma a ci gaba da zurfafa gyare gyare a fannin kiwon lafiya, ta yadda ba bukatar Sinawa su yi tafiya mai nisa domin samun jinya.
A jiya Talata, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya ziyarci gundumar Shaxian dake karkashin birnin Sanming, yayin rangadin da yake yi a lardin Fujian na gabashin kasar Sin, inda ban da asibitin, ya kuma yada zango a kauyen Yubang, da kuma cibiyar hada hadar hakkin mallakar hajojin gundumar Shaxian, inda ya ganewa idanun sa irin matakan da ake aiwatarwa, game da raya karkara da gyaran tsarin ikon mallakar gandayen daji. (Saminu)

SendShareTweetShare
Previous Post

Kalubalen Dake Gaban Shirin COVAX

Next Post

Kasar Sin Ta Gabatar Da Rahoto Game Da Keta Hakkin Dan-Adam A Amurka

RelatedPosts

Anya Japan Ta Damu Da Korafin Al’ummarta Da Na Sauran Jama’ar Da Shirinta Zai Yi Tasiri A Kansu?

Anya Japan Ta Damu Da Korafin Al’ummarta Da Na Sauran Jama’ar Da Shirinta Zai Yi Tasiri A Kansu?

by Sulaiman Ibrahim
13 hours ago
0

Daga CRI Hausa Kwararru daga bangarori daban daban na majalisar...

Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude Taron Boao Na Bana

Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude Taron Boao Na Bana

by Sulaiman Ibrahim
13 hours ago
0

Daga CRI Hausa A yau ne aka yi bikin bude...

Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ta Taimaka Wa Kasashen Da Ke Aiwatar Da Shawarar Farfado Da Tattalin Arziki

Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Ta Taimaka Wa Kasashen Da Ke Aiwatar Da Shawarar Farfado Da Tattalin Arziki

by Sulaiman Ibrahim
19 hours ago
0

Daga CRI Hausa Bayan da kasar Sin ta gabatar da...

Next Post
Kasar Sin Ta Gabatar Da Rahoto Game Da Keta Hakkin Dan-Adam A Amurka

Kasar Sin Ta Gabatar Da Rahoto Game Da Keta Hakkin Dan-Adam A Amurka

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version