Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Ya Auri Budurwarsa Bayan Ta Mutu Kan Sadaki 2,000 A Bauchi

by
1 year ago
in RIGAR 'YANCI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

Wani abu kamar almara ya faru a unguwar Abujan Kwara da ke cikin kwaryar Bauchi inda wani matashi mai suna Muhammad Salisu ya auri matacciyar budurwarsa mai suna Halima da suke zaune a unguwa daya a makon jiya.
Halima wacce ta rasu sakamakon gajeruwar rashin lafiyar da ta yi fama da shi. Bayan rasuwarta ne kuma aka daura mata aure da saurayinta da ta mace ta barci a wannan duniyar tare da alkawarin yin aure a tsakaninsu.
Auren ya dauru ne bayan da mutumin ya biya sadaki naira dubu biyu 2,000 ga iyalan mamaciyar budurwar tasa.
An nakalto cewa, marigayiyar budurwar ta taba shan alwashin cewa ita dai, ko bayan babu ranta, iyayenta su daura mata aure da Salisu (masoyinta).
Shi dai Salisu ya dauki tsawon lokaci yana soyayya da Halima wanda hakan ya kaisu ga yin alkawarin cewa ba za su taba rabuwa da juna ba har abada. Bayan jin dadi da ninkaya cikin kogin soyayya da suka yi na tsawon lokaci.
Da ya ke tabbatar da faruwar lamarin, Malam Bahajatu Nasir, ma’aikaci a hukumar Shari’ar Musulunci ta jihar Bauchi, ya yi bayanin cewa, auren ya wakana ne a lokacin da mahaifiyar marigayiya Halima ta sanar da jama’a cewa an shirya jana’iza da bizne marigayiyar.
Ya ce, Malamin da ya jagoranci daura auren shine Malam Abubakar wanda kuma tunin hukumar Shari’ar Musulunci ta kama shi bisa aikata hakan.
Da ya ke tofa albarkacin bakinsa kan wannan lamarin, wani Malamin addinin Islama a jihar Bauchi kuma Babban Limamin massallacin Jami’ar ATBU, Sheikh Mansur Isa Yalwa, ya misalta wannan auren a matsayin abun da bai dace ba kwata-kwata a addinin Musulunci.
A cewarsa, daga cikin matakan aure a Musulunci dole ne ma’auratan su kasance a raye, tare da karawa da cewa da zarar kuma daya daga cikinsu ya rasu, to zancen aure kuma ya kare.
“Don haka, ko auren ma da aka rigaya aka daura da zarar daya daga cikin ma’aurata biyu ya ko ta rasu, kai tsaye wannan auren ya rabu. Idan ta rasu, sai ka auri wata, in shine ya rasu sai ki auri wani. A batun da wani mutum ya auri wata matacciya, wannan auren ya saba wa koyarwar addinin Musulunci.”

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Marte: CATE Ta Jinjina Wa Sojojin Nijeriya Bisa Galaba Kan Boko Haram

Next Post

Shin Ya Kamata Real Madrid Ta Dogara Da Benzema Wajen Cin Kwallaye?

Labarai Masu Nasaba

Zamfara

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

by
1 year ago
0

...

Kansila Mai Mataimaka 18 Ya Sadaukar Da Albashinsa Na Farko

by
1 year ago
0

...

APC

Sanata Al-Makura Ya Cancanci Rike Kujerar Shugabancin APC, Inji Gwamna Sule

by
1 year ago
0

...

Kebbi

Bagudu Ya Bukaci ’Yan Nijeriya Su Zama Masu Kishin Kasa A Shafukan Sada Zumunta

by
1 year ago
0

...

Next Post
Benzema

Shin Ya Kamata Real Madrid Ta Dogara Da Benzema Wajen Cin Kwallaye?

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: