Ya Kamata A Lura Da Bukatun Kasashe Masu Tasowa
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata A Lura Da Bukatun Kasashe Masu Tasowa

bySulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
Kasashe

Na kan ga hotunan yin amfani da allunan sola da wasu abokanmu ‘yan Nijeriya suka watsa ta shafin Facebook: Wasu na amfani da na’urar a gida don tsimin kudin da ake kashewa. Wasunsu kuma sun bude tashohin cajin waya ta hanyar allunan sola, inda suka kaddamar da sana’ar kai.

Haka zalika, na taba karanta labarai game da yadda ake yawan aiki da allunan sola a kasashen Afirka. Misali, a kasar Zambia, ana gina wasu kauyuka masu fasahohin zamani bisa tushen fasahar allunan sola, inda ake aiki da allunan wajen samar da wutar lantarki, don biyan bukatun hasumiyar samar da sigina ga wayar salula, da makaranta, da karamin asibiti, gami da gidajen mazauna kauyukan, ta yadda aka shigar da manoma, wadanda ba su da damar amfani da wutar lantarki a baya, cikin wata sabuwar rayuwar zamani ta lantarki.

  • Sin Na Adawa Da Abubuwan Da Ke Da Alaka Da Ita A Cikin Sanarwar Taron Kolin Washington Na NATO
  • Shugaban IOC Ya Jinjinawa Burin Dandalin Wayewar Kan Bil Adam Na Nishan Mai Manufa Irin Ta Olympic

A zahiri, allunan sola sun baiwa mutane damammakin daidaita matsalar karancin wutar lantarki, da kyautata zaman rayuwa a kasashen Afirka. Kana yawancin allunan sola da suke amfani da su, an kera su ne a kasar Sin.

Bisa wata makala da Jaridar SCMP ta yankin Hong Kong na kasar Sin ta wallafa, an ce karfin samar da allunan sola na kamfanonin kasar Sin ya kai kashi 80% na jimillar karfin kamfanonin dake daukacin duniya. Kana yadda kamfanonin Sin ke kokarin rage kudin da ake kashewa domin samar da kaya, da inganta kaya a kai a kai, ya sa allunan sola da suke samarwa zama masu inganci da rahusa. Wannan ma dalili ne da ya sa allunan sola da fitilun sola, da sauran kayayyaki masu aiki da makamashin zafin rana, samun karbuwa a kasashen Afirka.

Sai dai duk wani abu, in dai akwai mai kaunarsa, to ba za a rasa mai kyamarsa ba. A ganin kasashen Turai da kasar Amurka, allunan sola da sauran kayayyakin makamashin sola na kasar Sin sun cika araha, abin da ya sanya allunan sola kirarsu kasa yin takara da na kasar Sin. Saboda haka suna cewa wai kasar Sin na “samar da kayayyaki fiye da kima”, da “ba da tallafi ga kamfanoni” da dai sauransu, har ma a bisa wadannan dalilai sun saka wa kasar Sin takunkumi. Misali, tun daga shekarar 2012, kasar Amurka ta riga ta kaddamar da haraji na hukunci kan allunan sola kirar kasar Sin.

Matakan takunkumi sun haifar da babban matsin lamba kan kamfanonin Sin, amma sun dukufa kan kirkiro sabbin fasahohi, da rage kudin da ake kashewa wajen kera kaya, gami da inganta kaya a kai a kai, ta yadda ake iya samar da kayayyaki masu inganci, da farashi mai rahusa, don biyan bukatun kasuwannin kasashe masu tasowa.

Wannan kokari da kamfanonin Sin suke yi ya sa bukatu kan allunan sola fara habaka tun bayan shekarar 2013, inda yawan allunan sola da aka kafa a kasashe daban daban ya karu da ninki 10 cikin wadannan shekaru da suka gabata. Yayin da kamfanonin kasar Sin masu kera allunan su ma suka samu damar jagorantar tsare-tsaren kera allunan sola na duniya, ta hanyar sabunta fasahohinsu a kai a kai.

A dayan bangaren kuma, kokarin kare sana’ar kera allunan sola da kasashen Turai da kasar Amurka suka yi ya bi ruwa. A kwanan baya, jaridar La Monde ta kasar Faransa, ta watsa wani rahoto game da Dalibor Nikolovski, wani dan kasuwa na kasar Faransa da ya kafa masana’antar kera allunan sola a kasar Sin. A cewar rahoton, tsarin masana’atun samar da kaya mai inganci na kasar Sin, da manufofin kasar na saukaka wa masu zuba jari aiki, da ba su gatanci, sun sa dan kasuwar kaunar kasar Sin, har ma ya dade yana zama a kasar har tsawon shekaru 17. Ko da yake hukumar kasar Faransa ta gayyace shi don ya koma gida ya kafa masana’anta a can, amma dan kasuwar ya ki yarda. A cewarsa, yin haka “ ba zai dace da sanin ya kamata ba”.

Hakika, dangane da allunan sola da sauran kayayyaki masu aiki da makamashi mai tsabta, ko ana samar da su “fiye da kima” ko akasin haka, bai kamata a yanke hukunci bisa matsin lambar da kamfanonin kasashen Turai da na Amurka ke fuskanta ba. Maimakon haka, ya kamata a lura da butakun kasashe masu tasowa, wadanda suke da rinjayen al’ummar duniya. A lokacin da mutane miliyan 600 dake nahiyar Afirka suka kasa samun wutar lantarki, kuma hukumomin nahiyar ke neman habaka tsare-tsaren samar da wutar lantarki ta zafin rana, don sanya karin mutane miliyan 300 na kasashen Afirka samun hidimomi masu alaka da wutar lantarki kafin shekarar 2030, kuma ake daukar matakan takunkumi don hana sana’ar kera allunan sola ta kasar Sin tasowa, a iya cewa wannan mataki bai dace da adalci ba ko kadan. Kana sam ba shi da amfani, wato ko kare kamfanonin cikin gida na kasashen Turai da na Amurka ma ya kasa, balle ma hana ci gaban harkokin kamfanonin Sin, wadanda ke biyan bukatun al’ummar kasashe masu tasowa.

Sai dai mun san su kasashen Turai da na Amurka, sun fara saka harajin kwastam na hukunci kan motoci kirar kasar Sin masu aiki da sabbin makamashi, to ko wane tasiri matakin zai haifar? Sai mu dubi abun da ya faru kan allunan sola domin gano amsar tambayar. (Bello Wang)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka
Ra'ayi Riga

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labaran Xinjiang A Zane: Manyan Sauye-Sauye A Fannin Ba Da Ilmi A Xinjiang

September 30, 2025
Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

Alfanun Harshen Mandarin A Kasashen Afirka

September 29, 2025
Next Post
Matsalar Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Sanya Dokar Takaita Zirga-zirgar Ababen Hawa

Matsalar Tsaro: Gwamnatin Zamfara Ta Sanya Dokar Takaita Zirga-zirgar Ababen Hawa

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version