Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Bayern Munchen Ta Dauki Zidane –Oliver Khan

by
3 years ago
in WASANNI
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Labarai Masu Nasaba

Mbappe Ya Ki Karbar Tayin Madrid, Zai Ci Gaba Da Zama A PSG

Chiellini Ya Bar Juventus

ADVERTISEMENT

Tsohon mai tsaron ragar kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munchen da kasar Jamus, Oliver Khan, ya bayyana cewa tsohon mai koyar da ‘yan wasan Real Madrid, Zinedine Zidane ne ya fi dacewa daya koyar da ‘yan wasan Bayern Munchen a kakar wasa mai zuwa.
Bayern Munchen dai za ta tsunduma neman mai koyarwa a karshen kaka sakamakon mai koyar da ‘yan wasan kungiyar na yanzu Nico Kobac zai iya barin kungiyar wanda hakan yasa Oliver Khan yake ganin Zidane yafi dacewa da aikin.
Khan ya ce Zidane zai dace da aikin saboda yanzu yaci kusan kowacce gasa kuma gashi yanzu baya tare da kowacce kungiya sakamakon barin Real Madrid da yayi a shekarar data gabata bayan ya ja ragarmar Real Madrid ta lashe kofin zakarun turai na uku a jere.
Ya kara da cewa Zidane mai koyarwa ne wanda yadace da kungiyar kwallon kafa ta Bayern Munchen da kuma tsarinta sosai kuma dayawa daga cikin ‘yan wasan kungiyar zasuji dadin aiki da Zidane saboda gogewarsa ta rike babbar kungiya.
A kwanakin baya dai Zidane ya nuna sha’awarsa ta komawa kungiyar Chelsea sai dai kawo yanzu har yanzu kungiyar ta Chelsea bata sallami kociyan nata ba, Mauricio Sarri wanda yake shan suka daga bangarori da dama daga kungiyar.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Da Dimi-Diminsa: Hukumar Zabe Ta Dakatar Da Zaben Jihar Ribas

Next Post

Real Madrid Ta Shirya Siyan Manyan ‘Yan Wasa A Kakar Wasa Mai Zuwa

Labarai Masu Nasaba

Mbappe Ya Ki Karbar Tayin Madrid, Zai Ci Gaba Da Zama A PSG

Mbappe Ya Ki Karbar Tayin Madrid, Zai Ci Gaba Da Zama A PSG

by
1 day ago
0

...

Chiellini

Chiellini Ya Bar Juventus

by Abba Ibrahim Wada
3 days ago
0

...

dambe

Wasan Damben Cin Mota: An Fara Fafatawa A Kano

by Abba Ibrahim Wada
1 week ago
0

...

klopp

Har Yanzu Ban Hakura Da Lashe Firimiya Ba, Cewar Klopp

by Abba Ibrahim Wada
1 week ago
0

...

Next Post

Real Madrid Ta Shirya Siyan Manyan ‘Yan Wasa A Kakar Wasa Mai Zuwa

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: