Ya Kamata Buba Marwa Ya Yaki ‘Yan Siyasa Masu Raba Wa Matasa Kwaya – Matasan Arewa A Kudu
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata Buba Marwa Ya Yaki ‘Yan Siyasa Masu Raba Wa Matasa Kwaya – Matasan Arewa A Kudu

bySulaiman
3 years ago
Arewa

Gamayyar Kungiyoyin Matasan Arewa da ke yankin Kudancin Nijeriya a Jihar Legas, ta yi kira ga shugaban Hukumar Yaki da Sha da Safarar Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA), Buba Marwa ya mike haikan wajen yaki da bata-garin ‘yan siyasa da ke raba kwayoyi ga matasa don ingiza su bangar siyasa.

A cewar gamayyar, bata-garin ‘yan siyasar suna amfani da kwaya wajen jirkita tunanin matasa don su cimma muradunsu na son zuciya.

  • Tattaunawa: Hulda Da Kasar Sin Muhimmin Ginshiki Ne Ga Ajandar Samar Da Abinci A Afrika

Shugaban Gamayyar Matasan, Alhaji Ibrahim Ya’u Galadanchi, wanda ya yi kiran a zantawarsa da manema labarai, ya kara da cewa, “Tun da yanzu an shiga lokacin siyasa gadan-gadan, bata-garin ‘yan siyasa suna nan babu abin da suke yi illa sayen miyagun kwayoyi suna raba wa matasa.

Don haka muke kira ga ga Shugaban NDLEA, Buba Marwa ya kara mikewa tsaye wajen sa ido a kan yadda wadannan bata-garin ‘yan siyasar suke amfani da kwaya su lalata tunanin matasa, su ingiza su cikin bangar siyasa don cimma burinsu.”

Wakazalika, gamayyar ta yi kira ga wakilan al’umma a majalisun dokoki a matakai daban-daban su kafa wata doka da za ta hana bangar siyasa, “Kuma muna kira ga sanatoci da ‘yan majalisar dokoki su ji tsoron Allah su yi dokar da za ta hana bangar siyasa domin ceton matasa.

Don babu ‘yan siyar da suke daukar ‘ya’yansu su je da su wajen taron siyasa domin gudun abin da zai je ya dawo. Wannan shi ne rokon da muke yi a gare su, domin amana ce suka dauka kuma Allah ba zai bar su ba sannan muna sake kira ga shugabanni musamman wadanda suka fito daka arewacin kasarmu su ji tsoron haduwarsu da Allah, domin sun san yadda yankinsu yake ciki, amma sun gaza yin abin da ya dace.”

Gamayyar ta kara da cewa, hatta su kansu ‘yan takarar shugaban kasa na jam’iyya mai mulki ta APC sun san ba a yi abubuwan da suka kamata wajen magance matsalar tsaron da ake fama da ita a kasar nan ba.

“Mun dade muna gaya wa wakilanmu da sauran shugabanninmu na arewa cewa ba a yin abubuwan da suka kamata wajen magance matsalar nan ta kashe-kashen jama’a. Ga shi yanzu hatta su kansu wasu daga cikin ‘yan takarar shugaban kasa na APC sun yi tsokaci a kan kashe-kashe da sace-sacen mutane da ake yi wanda gwamnati ba ta yi abin da ya dace ta yi ba na kawo karshen wadannan masifun. Mun tabbatar da cewa mutum daya ba zai iya ba dole sai an hada karfi da karfe.

“Dan haka muke kara kai kukanmu ga Ubangiji da ya ba mu shugabanni nagari wadanda za su hana yi mana kisan gillah kuma muna kira da gwamnatin Shugaban Kasa Muhammadu Buhari da ta yi dokar hana deligate a siyasar Nijeriya kafin ta sauka domin wannanma zai taimaka wa alumma.

“Haka nan muna kara kiga ga matasa su kula saboda sun ga yadda tsarin siyasarmu yake, ba a kulawa da su sai in za a saka su bangar siyasa a ba su kwaya.” In ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Next Post
Mayakan Ukraine Na Gudu Daga Fagen Fafafata Wa Da Rasha

Mayakan Ukraine Na Gudu Daga Fagen Fafafata Wa Da Rasha

LABARAI MASU NASABA

…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version