Rabiu Ali Indabawa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Ya Kashe Mata Da Yaro Da Shebur

by Rabiu Ali Indabawa
January 28, 2021
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

A yau aka kama wani mutum mai shekaru 28, Chukwuemeka Obijofa da ake zargi da kashe matarsa da danta mai shekaru hudu a kauyen Ofufe Nza da ke karamar Hukumar Ekwusigo a Jihar Anambra. An rahoto cewa wanda ake zargin ya aukawa matar, Chisom da dansa, Amanda a kawunansu da shebur.

Jaridar Nation ta tattaro wanda ake zargin ya kuma raunata wani dan banga da ya yi kokarin ceton wadanda abin ya shafa da wannan abin. Da yake tabbatar da faruwar lamarin, kakakin rundunar ‘yan sanda, Haruna Mohammed ya ce an cafke wanda ake zargin yayin da aka ajiye gawarwakin a dakin ijiye gawarwaki na asibitin bayan likita ya tabbatar da cewa sun mutu.
Ya ce: “A ranar 27/1/2021 da misalin karfe 7:45 na yamma,‘ yan sanda da ke aiki a ofishin ‘yan sanda na Ozubulu, sun cafke wani Chukwuemeka Obijofa, mai shekara 28, na kauyen Ofufe Nza da ke karamar Hukumar Ekwusigo ta Jihar Anambra. “Wanda ake zargin ya gudu a cikin wani yanayi amma an gano shi bayan da ya auka wa matar sa, Chisom Chukwuemeka,‘ yar shekaru 26, da kuma danta mai suna Amanda Chukwuemeka, dan shekaru 4, dukkansu an samu shedar guda, tare da su ta duka da shebur a kawunansu.
“Wanda ake zargin ya yi amfani da abu guda kuma ya raunata wani dan banga wanda ya yi kokarin ceton wadanda abin ya shafa.
“Jami’an ‘yan sanda sun ziyarci inda lamarin ya faru inda suka garzaya da wadanda lamarin ya rutsa da su zuwa asibitin hadin gwiwa, Ozubulu, domin kula da lafiyarsu inda likitocin suka tabbatar da cewa maman ta ‘ya’ya da danta mutu.
“Yan banga da suka samu rauni suna asibiti suna karbar magani, yayin da aka ijiye gawarwakinsu a dakin ijiye gawarwaki na asibiti don gudanar da bincike.”
Mohammed ya kara da cewa, kwamishinan ‘yan sanda, John Abang ya umarci DPO da ya tura lamarin zuwa ofishin CID na jihar a Awka, domin gudanar da bincike cikin tsanaki don gano hakikanin abin da ya faru.

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Abubuwan Da Suka Biyo Bayan Canja Shugabannin Tsaron Nijeriya

Next Post

Gwamnan Zamfara Ya Ja Kunnen Masu Labaran Karya A Kafafen Sada Zumunta

RelatedPosts

An Sako Daliban Da Aka Sace A Zamfara

An Sako Daliban Da Aka Sace A Zamfara

by Rabiu Ali Indabawa
54 mins ago
0

Rahotanni daga jihar Zamfara sun tabbatar da cewa an ceto...

IITA Ta Fara Horas Da Matasa Sana`o`in Dogaro Da Kai A Zariya

IITA Ta Fara Horas Da Matasa Sana`o`in Dogaro Da Kai A Zariya

by Rabiu Ali Indabawa
2 days ago
0

Daga Nasiru Adamu Cibiyar kula da albarkatun aikin gona ta...

Garkuwa Da Dalibai: An Ceto Daliban Kagara, Ana Cigaba Da Neman Na Jangebe

Garkuwa Da Dalibai: An Ceto Daliban Kagara, Ana Cigaba Da Neman Na Jangebe

by Rabiu Ali Indabawa
2 days ago
0

Daga Muhammad Awwal Umar, Minna Da sanyin safiyar asabar din...

Next Post
Gwamnan Zamfara

Gwamnan Zamfara Ya Ja Kunnen Masu Labaran Karya A Kafafen Sada Zumunta

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version